Friday, December 5
Shadow

Gwamnatin Jihar Akwa-Ibom ta tilastawa ma’aikatan Lafiya shiga jarjejeniya da rantsuwa cewa idan ta dauki nauyinsu suka yi karatu ba zasu tsere zuwa kasashen waje ba

Gwamnatin jihar Akwa-Ibom ta bukaci ma’aikatan lafiya a jihar da su sha rantsuwa cewa ba zasu tsere ba idan ta dauki nauyinsu suka je suka yi karatu.

Shugaban ma’aikatan jihar, Elder Effiong Essien ne ya bayyana hakan inda yace zasu dauki ma’aikatan lafiya 600.

Yace wannan bukata dolece saboda a tabbatar da cewa ma’aikatan lafiyar sun gudanar da aiki daidai da yawan kudin karatun da aka kashe a kansu.

Karanta Wannan  TIRƘASHI: Añ bankado Natasha na wasa da hankalin jama'a ne kawai game da zargin Akpabio?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *