Saturday, December 13
Shadow

An kama Barawo bayan da ya saci Keke Napep a masallaci a jihar Naija

Hukumar ‘yansandan jihar Naija sun yi nasarar kama wani barawon Keke Napep a jihar.

Kakakin ‘yansandan jihar, SP Wasiu Abiodun ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace lamarin ya farune ranar 5 ga watan April.

Sunan Barawon da aka kama Abdulaziz Salisu kuma yayi satar ne yayin sallar Asuba a Dakwa.

Yace bayan ya saci Keke Napep din yayi yunkirin kaiwa wani me suna Abubakar Mohammed dan ya sayar masa dashi.

Yace ana tsaka da sallah ne Abdulaziz ya fita ya sace Keke Napep din amma sai ‘yansanda suka kamashi a gadar Maje inda ya amsa cewa satota yayi.

Karanta Wannan  Nan da shekarar 2050 yawan 'yan Najeriya zai karu kuma matsalar tsaro da hakan zai iya haifarwa yafi wanda ake ciki yanzu>>Tsohon Shugaban kasa, Obasanjo yayi gargadi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *