Friday, December 5
Shadow

Sarkin Saudiyya, Salman bin Abdulaziz Al Saud ya ce a dauko Falasdiynawa 1000 wanda aka kàshè ‘yan uwansu, ko aka jikkata ‘yan uwansu ko aka kama ‘yan uwansu a kaisu su yi aikin Hajji Kyauta, zai biya kudin daga Aljihunsa

Me alfarna sarkin Saudiyya Salman bin Abdulaziz Al Saud ya bayar da umarnin dauko Falasdiynawa 1000 a kaisu aikin Hajji kyauta zai biya kudin daga Aljihunsa.

Yace a zabo wadanda aka kashewa ‘yan uwa ko aka jikkata musu ‘yan uwa ko aka kama ‘yan uwansu sune zai dauki nauyi.

Ba wannan ne karin farko da Sarkin ya taba yin irin wannan abu ba, ko da a shekarun 2023 da 2024 duk ya bayar da irin wannan tallafi.

Kasar Israyla dai ta kashe Falasdiynawa da yawa a ci gaba da yakin da tace tana yi da kungiyar Hàmàs.

Salman bin Abdulaziz Al Saud

Karanta Wannan  Giya ce dalili na 3 na kamuwa da cutar daji(cancer)

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *