Friday, December 5
Shadow

APC ta zargi cewa ‘yan Adawa ne ke daukar nauyin harè-hàrèn da ‘yan Bìndìgà ke kaiwa dan kawai ace Tinubu bai iya mulki ba baya kokari

Jam’iyyar APC, ta yi zargin cewa, Wasu ‘yan Adawa ne ke daukar nauyin ‘yan Bindigar dake kai munanan hare-hare a fadin Najeriya dan a karya lagon Gwanatin shugaba Tinubu.

Hakan ya fito ne daga bakin daya daga cikin masu ruwa da tsaki na APC a jihar Osun, retired Brig.- Gen. Bashir Adewinbi.

Saidai yace shugaba Tinubu ya tashi tsaye haikan yana kokarin magance wannan matsala.

Ya bayyana hakane yayin wata ziyara da mata ‘yan APC suka kai masa.

Yace gwamnatin Tinubu na son amfani da makamai na zamani dan magance matsalar tsaron da ake fama da ita.

Karanta Wannan  Sheikh Ibrahim Ɗahiru Bauchi Ya Jagoranci Tawagar Kungiyar Mu'assasa Domin Yiwa Gwamna Raɗɗa Ta'aziyyar Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *