Friday, December 5
Shadow

‘Yan sanda basu kama mutane saboda zagin ‘yan siyasa, har ni ku zaga babu wanda zai kamaku>>Inji Shugaban ‘yansandan Najeriya, IGP Kayode Egbetokun

Shugaban ‘yansandan Najeriya, IGP, Kayode Egbetokun ya bayyana cewa, ‘yansanda basa kama mutum dan kawai ya zagi ko sukar dan siyasa.

Yace koshi ana zaginshi a kafafen sada zumunta amma hakan baya sawa a kama mutane.

Ya bayyana hakane ranar Talata a wajan wani taron da aka gudanar a Abuja inda yace amma inda za’a iya kama mutum shine idan ya wallafa labaran karya.

Yace ko da ba akan dan siyasa ba idan mutum ya wallafa labaran karya za’a iya hukuntashi.

Karanta Wannan  Hotuna: EFCC Ta Kama Masu Zamba a Yanar Gizo 120, Ta Kwato Motoci Masu Tsada a Jihar Legas

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *