Friday, June 26
Shadow

Fada ya kare tsakanin mu, mun shirya>>Wike da Fubara bayan da Shugaba Tinubu ya sasantasu

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya bayyana cewa a yanzu babu sauran rashin jituwa tsakanisa da dakataccen gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara.

Ya bayyana hakane bayan ganawar da suka yi da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da daren ranar Alhamis.

Wike yace komai ya wuce.

Shima Fubara ya bayyana cewa zaman lafiya ya dawo jihar Rivers inda ya bayyana jin dadinsa da ganin wannan rana da suka yi sulhu shi da Wike.

Karanta Wannan  Bidiyo: An yi kuskuren turawa Fasto Naira Miliyan 1 mimakon dubu dari a matsayin sadaka saidai da aka ce ya mayar da kudin, yace Kudin da aka baiwa Yesu sadaka ba'a mayar dasu, me kudin ya kira 'yansanda

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *