Friday, December 5
Shadow

Hukumar JAMB ta fitar da Jadawalin Jihohin da aka fi yin satar amsa, Duba kaga ko jiharka na ciki

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[“local”],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Hukumar shirya jarabawar Jami’a ta JAMB ta sanar da jihohin Anambra da Imo a matsayin wadanda aka fi yin satar amsa.

A bayanan da hukumar ta fitar ranar Talata ta fitar da cibiyoyin da aka kama ana satar amsa a cikinsu.

Gaba daya an kama Cibiyoyi 19 ne a fadin Najeriya.

A jihar Anambra ne aka fi kama masu yawa inda ake da guda 6, Sai guda 4 da aka kama a jihar Imo, An kama guda daya a Abia, hakanan an kama guda daya a Edo.

A jihar Kano guda 2 aka kama.

sai guda 1 da aka kama a kowane jihohin, Ebonyi, Delta, Kaduna, Rivers da Enugu.

Shugaban hukumar JAMB din, Prof. Ishaq Oloyede ne ya bayyana hakan.

Karanta Wannan  Ya Zama Wajibi Ga Ƴan Nijeriya Mu Tashi Tsaye Wajen Ganin An Kawar Da Gwamnatin APC 2027 A Kowane Matakai, Saboda Mawuyacin Halin Da Ta Jefa Mu, Ta Hanyar Haɗaka Da Muke Shirin Kafawa Nan Gaba Kaɗan, Cewar Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Dakta Mustapha Inuwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *