Tuesday, April 7
Shadow

Hukumar JAMB ta fitar da Jadawalin Jihohin da aka fi yin satar amsa, Duba kaga ko jiharka na ciki

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[“local”],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Hukumar shirya jarabawar Jami’a ta JAMB ta sanar da jihohin Anambra da Imo a matsayin wadanda aka fi yin satar amsa.

A bayanan da hukumar ta fitar ranar Talata ta fitar da cibiyoyin da aka kama ana satar amsa a cikinsu.

Gaba daya an kama Cibiyoyi 19 ne a fadin Najeriya.

A jihar Anambra ne aka fi kama masu yawa inda ake da guda 6, Sai guda 4 da aka kama a jihar Imo, An kama guda daya a Abia, hakanan an kama guda daya a Edo.

A jihar Kano guda 2 aka kama.

sai guda 1 da aka kama a kowane jihohin, Ebonyi, Delta, Kaduna, Rivers da Enugu.

Shugaban hukumar JAMB din, Prof. Ishaq Oloyede ne ya bayyana hakan.

Karanta Wannan  Cikakken rahoto kan irin mummunar barnar da kasar Israyla tawa kasar Ìràn a hàrè-hàrèn da ta kai mata, harin ya kàshè fararen hula da dama, an gano karin manyan sojoji da masana kimiyya da harin ya kàshè

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *