
Matashiya me sunan Sister Zeerah wadda shahararriya ce a Tiktok ta bayar da labarin abinda ya faru da ita bayan da aka kamata a ofishin ‘yansanda saboda ta yi murnar mutuwar Buhari.
Tace har gida ‘yansanda suka je suka dauko ta.
Tace da suka je ofishin ‘yansanda aka ce mata anata kiransu akan su dauki mataki akanta.
Tace nan wani yayi ta zaginta, aka ce ta cire hijabinta, dama bata da dankwali, sai Hijabi da doguwar riga.
Tace bayan ta cire hijabin kuma yace ta cire doguwar rigar tace masa idan ta cire doguwar rigar zata zama tsirara saboda bata da komai a cikin jikinta bayan rigar, yace shi ba ruwansa uban wa yace ta zagi matacce?
Tace anan dai ta kwana amma daga karshe an bada belinta akan Naira dubu 50.
Lamarin ya dauki hankula sosai.