Monday, April 6
Shadow

Wata Sabuwa: Sowore ya zargi ɗansanda da sace masa gilashi a wajen zanga-zangar ƴansanda

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Dan gwagwarmayar kare hakkin ɗan’adam kuma tsohon dan takarar shugaban kasa, Omoyele Sowore, ya zargi wani ɗansanda da sace masa gilashin da mai ɗauke da na’ura a wajen zanga-zangar da aka yi a hedikwatar ƴansanda a Abuja a yau Litinin.

Zanga-zangar, wacce Sowore tare da wasu masu fafutukar kare hakkin bil’adama da tsoffin jami’an ‘yan sanda suka jagoranta, ta nemi a inganta walwalar jami’ai da kuma cire tsoffin jami’an daga tsarin fansho na haɗaka.

Daily Trust ta rawaito cewa a wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta , Sowore ya bayyana cewa jami’in, wanda ke cikin kayan fararen hula, an kama shi a bidiyo yana aikata laifin.

Karanta Wannan  Dr. Ahmad Gumi ya bukaci gwamnatin Tinubu ta nemi Trump ya janye barazanar da yawa Najeriya idan kuma yaki janyewa Najeriya ta yanke alakar jakadanci da Amurka

“Wannan jami’in rundunar ‘yansanda na Najeriya, cikin kayan fararen hula, ya sace min gilashin AI Rayban a hedikwatar rundunar yayin #ZangaZangarYanSanda yau. Manyansa suna kare shi. Don Allah a turo min saƙo idan kun san sunansa da mukaminsa cikin gaggawa!” in ji Sowore.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *