Friday, December 5
Shadow

Kaine Zabin Kanawa a 2027, Jam’iyyar APC reshen jihar Kano ta baiwa shugaba Tinubu tabbaci

Jam’iyyar APC Reshen jihar Kano ta baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu tabbacin goyon baya a zaben shekarar 2027 me zuwa.

Jam’iyyar ta kuma bayyana Dr. Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar a jihar.

Sun bayyana hakane yayin wani zama da aka yi a gidan tsohon shugaban jam’iyyar na kasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

Shugaban jam’iyyar a jihar, Alhaji Abdullahi Abbas ya bayyana cewa, an shirya taronne dan warware matsalolin cikin gida na jam’iyyar da kuma shiryawa babban zaben shekarar 2027 dake tafe.

Karanta Wannan  Allah Sarki Kalli Hotuna: Wasu daga cikin daliban Jihar Kebbi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *