Friday, January 23
Shadow

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu a 2027

Babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi mambobinta da ke nuna goyon bayan sake zaɓen Shugaba Tinubu na APC a 2027.

Cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran jam’iyyar Hon. Debo Ologunagba ya fitar, PDP ta bayyana hakan da ta ce wasu mambobinta na yi a matsayin yi mata zagon-ƙasa.

”Abin taƙaici ne abinda wasu mambobinmu ke yi a kafafen yaɗa labarai, inda maganganunsu da ayyukansu ke nuna goyon baya ko yin wani abu da bai wa ɗan takarar APC nasara a zaɓen 2027,” a cewar sanarwar.

PDP ta ce hakan ya saɓa wa dokokin da suka kafa jam’iyyar, kuma barazana ce ga ci gaba da wanzuwar jam’iyyar.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Kalli Bidiyon yanda aka Dambhace aka baiwa hammata iska tsakanin jami'an tsaron gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed da jami'an tsaron da aka Jibge dan su hana Gwamnan shiga Hedikwatar Jam'iyyar PDP

Jam’iyyar ta kuma ce hakan zai kawo tarin matsalolin da za su haifar da rarrabuwar kawuna a cikinta, wanda kuma cewarta idan ba a magance su ba za su janyo wa jam’iyyar rashin nasara a zabukan da ke tafe.

Kan haka ne PDP ta yi gargadin sanya takunkumai masu tsauri ga mambobinta da aka kama da wannan laifi.

Yanzu haka dai Nyesom Wike – wanda babban jigo ne a jam’iyyar ta PDP – na cikin ƙunshin ministocin Shugaba Tinubu na APC.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *