Thursday, April 9
Shadow

Hoto: An kamashi da ka-wu-nan mutane 8 dan yin tsafi

Jami’an ‘yansanda a jihar Ondo sun kama wani matashi me suna Yusuf Adinoyi bayan samunsa da kawunan mutane 8.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Abayomi Oladipo, ya tabbatar da kamen inda yace an kama wanda ake zarginne ranar Litinin bayan an kafa shingen bincike.

Mutumin na kan hanyar zuwa Akure ne kamin aka tare motarsu wadda yayi kokarin tserewa amma aka bishi aka kamoshi.

Ya amsa laifinsa inda yace a baya yana sana’ar sayar da manja ne amma rashin lafiyar mahaifiyarsa tasa ya shiga harkar sayar da kawuna.

Yace wannan ne karo na 3 da yake son sayar da kawunan inda a farko ya sayar da guda 4, sannan ya sayar da guda 3 hakanan sai yanzu zai sayar da guda 8.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Tun ina Yarinya 'yar Shekara 5 na gano karyar da ake mana a coci, daga nan na ji soyayyar Annabi Muhammad(Sallalahu Alaihi Wasallam) ta shiga Raina kuma na zabeshi a matsayin Masoyi, Munirat Abdulsalam ta gayawa Kiristoci masu ce mata ta koma Kirista

Kwamishinan ‘yansandan yace za’a gurfanar dashi a kotu bayan kammala bincike.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *