Friday, December 5
Shadow

Jam’iyyar APC ta lashe zaben cike gurbi na Ghari/Tsanyawa, Kano

Rahotanni sun tabbatar da cewa, Jam’iyyar APC ta lashe zaben cike gurbi na Ghari/Tsanyawa, Kano.

Baturen zabe, Professor Muhammad Waziri na jami’ar Bayero dake Kano ne ya bayyana Garba Gwarmai na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri’u 31,472.

Yayi nasara ne akan dan takarar jam’iyyar NNPP, Yusuf Maigado, wanda ya samu kuri’u 27,931.

Karanta Wannan  Ina hada 2.4m duk shekara a harkar bara - Habib Ibrahim

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *