Friday, December 5
Shadow

Mun raba kudin Talli Naira Biliyan 330 ga gidaje Miliyan 8.5 a Najeriya>>Inji Ministan kudi

Gwamnatin tarayya tace ta rabawa gidaje Miliyan 8.5 Tallafin kudi Naira Biliyan 330 a fadin Najeriya.

Ministan kudi, Wale Edun ne ya bayyana hakan.

Ya bayyana hakane ranar Laraba a Abuja inda yace gwamnati ta dawo da raba tallafin bayan Gyare-Gyaren da aka wa tsarin.

Yace suna raba kudadenne saboda ragewa mutane radadin tsadar rayuwa inda yace mutane Miliyan 15 suke son rabawa.

Yace zuwa yanzu sun raba kudin a gide Miliyan 8.5 inda suke biyan Naira dubu shirin da biyar duk wata.

Ministan yace sauran ma zuwa karshen shekarar nan za’abasu.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Ganin Tankokin dakon Man Fetur na Dangote sun rikita wasu 'yan Kudu suna ta kukan cewa, zai mamaye ko ina

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *