Friday, December 5
Shadow

Nine na roki Shugaba Tinubu ya yafe mata, saboda yanke mata hukunci ba zai dawo da dana ba>>Inji Mahaifin Mijin Maryam Sanda

Mahaifin mijin Maryam Sanda, Alhaji Ahmed Bello Isa ya bayyana cewa, shine ya roki shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yafewa matar dansa duk da itace ta kashe dan nasa.

Alhaji Ahmed Bello Isa yace aiwatarwa da Maryam Sanda hukuncin kisa ba zai dawo da dansa,Bilyaminu Bello ba.

Yace maimakon haka ya zabi yafe mata dan a saketa ta kula da ‘ya’yanta kanana.

Ya bayyana hakane yayin ganawa da manema labarai a Abuja ranar Talata wadda suka gudanar shi da mahaifin Maryam Sanda, Alhaji Garba Sanda

Karanta Wannan  Hotuna:Rahama Sadau tawa masoyanta gaisuwar barka da sabon wata

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *