Friday, December 5
Shadow

Lura da irin Arzikin da Allah yawa Najeriya, bai kamata akwai talaka a kasarnan ba>>Inji Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, Lura da irin Arzikin ma’adanan karkashin kasa da Allah yawa kasarnan, bai kamata ace akwai talaka a kasarba

Shugabab ya bayyana hakane a wajan taro kan Arzikin ma’danan karkashin kasa da Allah yawa Najeriya da ya gudana a Abuja.

Sakataren Gwamnatin tarayya, George Akume ne ya wakilci shugaban kasar a wajan taron.

Ya bayyana cewa, Gwamnatin tarayya zata yi dukkan mai yiyuwa wajan samar da yanayi me kyau na zuba hannun jari a kasarnan ta bangaren ma’adanan karkashin kasa.

Sannan ya yi kira ga kasashen Afrika dasu yi amfani da ma’adannan karkashin kasar da Allah ya hore musu dan karfafa tattalin arzikin su.

Karanta Wannan  Gaba daya na makance na daina gani bayan dana biyewa Snoop Dog muka sha wiwi>>Inji Mawaki Ed Sheeran

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *