Wednesday, April 8
Shadow

Daga yanzu karku kara yadda, Duk wanda aka yi Gharkiwa dashi ya biya kudin Fhansa ya kai Gwamnati kara ta biyashi kudinsa>>Inji Lauya Femi Falana

Babban lauya, Femi Falana(SAN) ya baiwa ‘yan Najeriya shawarar cewa, kar su sake yadda daga yanzu duk wanda aka sake yin Garkuwa dashi ya biya kudin fansa, ya kai Gwamnati kara ta mayar masa da kudinsa.

Yace dalili kuwa shine, Gwamnatin ta kasa bisa hakkin dake kanta na samar da tsaro ga ‘yan kasa dan haka ya kamata a kalubalanceta.

Ya bayyana hakane a wajan wani taro da ya gudana a jami’ar Yakubu Gowon University dake Abuja.

Karanta Wannan  Matar data daina cin duk wani abu da aka dafa sai kayan itace ta rigamu gidan gaskiya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *