Saturday, December 20
Shadow

Zafa mu buga gasar cin kofin Duniya ta 2026>>Inji hukumar kwallon Najeriya

Hukumar kula da wasanni ta kasa, NSC ta bayyana cewa Kasar Dr. Congo ba zata tsallake korafin da aka shigar akanta na maganar saka ‘yan wasan da basu dace ba a wasannin data buga da Najeriya.

Shugaban hukumar, Shehu Dikko ne ya bayyana hakan a yayin ganawa da gidan Talabijin na Arise TV.

Yace ba wai dan Najeriya bata yi nasara bane yasa yake fadat hakan ba, yace tun kan a buga wasan sun san cewa wasu ‘yan wasan kasar ta Benin Republic basu cancanta da buga wasan ba.

Najeriya dai ta shigar da kara gaban FIFA inda take neman a binciki Dr. Congo kan ‘yanwasanta.

Karanta Wannan  Wani Dan Kabìlar Ibo Keñan Da Ya Karbi Musùĺùnci A Sansanin Masu Bautar Kasa Dake Garin Karaye A Kano, Inda Ya Sauya Sunansa Zuwa Yusuf

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *