Saturday, December 27
Shadow

Ba kasarka ta UAE ba, Musulunci ya riga zuwa Afrika kamin ya je Madina>>Gimba Kakanda ya mayarwa da Balarabe da yace a wajansu Bakaken Fata suka koyi Addini Martani

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Wani Balarabe da ya yiwa wani dan Najeriya gorin cewa a wajansu aka koyi addini, ya sha raddi daga wajan Gimba Kakanda.

Wani dan Najeriya ne ya nuna rashin jin dadi game da yanda kasar UAE ta taya Kiristoci murnar Kirsimeti.

Balaraben dan kasar ta UAE wanda ke amfanin da sunan Imam of Peace ya cewa dan Najeriyar ya kyalesu dan a wajansu aka koyi addinin Musulunci.

Saidai Gimba Kakanda yace masa Musulunci ya riga zuwa Afrika kamin yaje Madina ballantana ma kasarsa ta UAE.

Yace Musulunci ya je Ethiopia a wajan Sarki Najashi kamin ya je Madina.

Sannan kuma Allah yana kallon zuciya ne ba kabila ko kala ko kudi ba, wanda yafi jin tsoronsa shine wanda yafi kusanci dashi.

Karanta Wannan  Innalil-Lahi wa'inna iLaihi rajiun: Allah ya yiwa dalibai almajirai (17) Rasuwa Agarin Kauran-Namoda sanadiyyar Gobara wadda ta shafe awa uku tana ci

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *