Friday, June 26
Shadow

Da Duminsa:Hukumar zabe me zaman kanta INEC ta sanar da ranar da za’a yi zaben shugaban kasa na shekarar 2027

Hukumar zabe me zaman kanta INEC ta sanar da ranar 20 ga watan Fabrairu na shekarar 2027 a matsayin ranar da za’a gudanar da zaben shugaban kasa na shekarar 2027.

Shugaban Hukumar zaben, Professor Joash Amupitan ne ya bayyana haka ga manema labarai a Abuja ranar Juma’a.

Yace zaben shugaban kasa dana ‘yan majalisun tarayya za’a yishi ne ranar 20 ga watan Fabrairu inda kuma zaben Gwamnoni dana ‘yan majalisar jihohi za’a yishi ne ranar 6 ga watan Maris.

Ya bayyana cewa, sun shirya tsaf dan gudanar da zaben.

Karanta Wannan  An dauke Wuta a wani sashe na kasar Amurka inda sama da mutane 300,000 suka fada Duhu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *