
Wannan wata mata ce da aka baiwa tallafin Gwamnatin tarayya na Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu na kayan Azumi.
Bayan karbar kayan, ta yi fatan cewa, duk wanda baya son shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya zarce a shekarar 2027 Allah yasa ya rasu.
Saidai da yawa sun yi Allah wadai da hakan inda wasu ke tambayar duk kwana nawa abincin zai mata?