
Wata Kirista Dalibar Jami’ar Kaduna Polytechnic dake Kaduna ta koka da cewa ba’a musu Adalci inda tace sun saka kaya basu nuna komai na tsiraici ba amma an hanasu shiga makaranta.
Ta koka da cewa, Ana tilasta musu rufe jikine saboda musulmai dake Azumin watan Ramadana.
Tace wannan ba adalci bane.
Dalibar ta bayyana hakane a Bidiyon data yi a kofar makarantar bayan da aka hanasu shiga inda ta yi kira ga hukumomin makarantar su dauki mataki.