
Wasu da ba’a san ko su wanene ba sun raba matashi me sharhi a kafafen sada zumunta, Khalil dan Shagamu da Duniya a gidansa dake Kano.
Dan Shagamu kamin barinsa Duniya yayi wani Bidiyo inda yake kira ga Hukumomi cewa ‘yan Izala na farautar rayuwarsa inda aka ji yana kiran sunayen Gwamnan Kano da wasu malamai.

Wannan Bidiyon ya dauki hankula sosai bayan rasuwarsa inda ake ta watsa shi a kafafen sada zumunta.
Hakanan kungiyar Amnesty international dake ikirarin kare hakkin bil’adama tace ya kamata Gwamnatin tarayya ta dauki matakin hana asarar rayuka.
Sannan ta yi Allah wadai da abinda akawa Danshagamu.
Hakanan Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumomi da su kamo wadanda suka aikata wannan rashin Imani.
Tuni dai aka kama mutane biyu da ake zargi da yin wannan ta’asa.