Saturday, September 12
Shadow

Dan kwallon Najeriya, Ademola Lookman ya shiga jerin wanda zasu iya lashe kyautar Ballon D’ Or

Dan kwallon Najeriya, Ademola Lookman ya shiga jerin ‘yan wasan da zasu iya lashe kyautar Ballon D’ Or ta shekarar 2014.

Lookman ya shiga jerin manyan ‘yan kwallon Duniya irin su Bellingham, Kylian Mbappe da Vinicius Jr wanda ke gaba-gaba wajan lashe kyautar.

Dan wasan yayi kokari sosai a gasar Serie A inda ya ciwa kungiyarsa ta Atalanta kwallaye 3 a wasan da suka buga da Bayer Leverkusen a gasar Europa.

Hakanan a gasar AFCON,ya ciwa Najeriya kwallaye 3.

A baya dai an yi rade-radin zai koma kungiyoyin Arsenal da PSG saidai a karshe be bar kungiyar tasa ba.

Karanta Wannan  Abin yabi Jikinta: Maryam Yahya ta sake sakin sabbin Hotuna da Bidiyo babu rigar Mahmah duk da cece-kuce da mutane ke yi akan hakan

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *