Friday, May 15
Shadow

Kalli Bidiyo da hotuna yanda motar Dangote ta buge mutane 3 suka mùtù a Jihar Legas

Hukumar kula da ababen hawa ta jihar Legas, LASTMA ta tabbatar da mutuwar mutane 3 bayan da motar Dangote ta bugesu.

Rahoton Daily Post yace motar Dangoten dake tafiya akan titin Ita-Opo, Epe ta samu matsalar birki ne inda hakan yasa ta yi taho mu gama da wasu motocin.

Shugaban hukumar ta LASTMA, Olalekan Bakare-Oki ya tabbatar da faruwar lamarin ta bakin kakakin hukumar Taofiq Adebayo, yace motar ta Dangote ta buge Keke Napep da wata mota dake ajiye a gefe.

Karanta Wannan  Ana tsaka da min Tiyata a Asibiti, sai na ji na Mutu, kuma na hadu da Jesus har ya nuna min Aljannah>>Inji Wannan Mutumin

Yace direban keke Napep din da dalibai biyu daga makarantar Manpower Technical School sun mutu sanadiyyar hadarin

Karanta Wannan  Ku kiyayi kanku da tunanin fita kasar waje ci rani, da yawa da suka je suna cikin nadama>>Gwamnati ta gargadi Matasa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *