Thursday, February 5
Shadow

Hotuna: Matar aure ta càkàwà mijinta wuka ya mùtù bayan da gardama ta barke tsakaninsu

Wata matar aure me suna Comfort Olajumoke Olalere Tinubu ta kashe mijinta ta hanyar caka masa wuka ya mutu bayan da gaddama ta barke a tsakaninsu.

Lamarin ya farune a Gbeyi dake yankin Adegbayi a Ibadan jihar Oyo da misalin karfe 10 na daren Laraba, 30 ga watan October 2024.

Shekaru 3 kenan da aurensu kuma suna da yara 2.

TheNation ta ruwaito cewa matar me shekaru 33 ta kulle mijinta, Olusegun a dakinsu bayan da suka yi fada wanda daga baya abin ya kazance da ya kai ga har ta caka masa wuka ya mutu.

Zuwa yanzu dai ‘yansanda na bincike akan lamarin.

Karanta Wannan  Har Majalisa Sanata Natasha Akpoti ta zo mana da Mijinta suka sumbaci juna, su rasa inda zasu je su yi hakan sai a gaban mu, Tana zargin Sanata Godswill Akpabio da nemanta ne kawai dan daukar hankalin mutane>>Inji Majalisar Dattijai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *