Friday, December 5
Shadow

Na karbi mulki Najeriya na cikin wahala da matsin tattalin arziki shiyasa na dage dan kawo gyara>>Shugaba Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, ya karbi mulkin Najeriya a yayin da take cikin wahalar rashin tabbas na tattalin arziki.

Shugaban yace shiyasa ya dauki matakai tsaurara musamman a bangaren kudi dan ganin ya kawo ci gaba.

Shugaban ya bayyana hakane a wajan rantsar da zababben gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo inda mataimakinsa, Kashim Shettima ya wakilceshi.

Yace a yanzu saboda matakan da ya dauka, kasar ta dauki hanyar ci gaba da nasara.

Karanta Wannan  YANZU-YANZU: Duk Wanda Ya Taimakawa Sòjin Nàjeriya Da Bayanaɲ Sirri Wajen Ganin An Kawo Ƙarshen Ƴan Biɲdíĝa, Zamu Bashi Kyautar Miliyan 20, Céwar Ƙarmin Ministan Tsaro Bello Matawalle

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *