Wednesday, March 18
Shadow

A yau shugaba Tinubu zai sakawa sabbin dokokin Haraji hannu

A yau, Alhamis ne ake sa ran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai sakawa sabbin kudirin dokokin Haraji hannu a fadarsa dake Abuja.

Hakan na kunshene cikin sanarwar da kakakin shugaban kasar, Bayo Onanuga ya fitar.

Kudirin dokokin guda 4 ne wanda tuni majalisar tarayya ta amince dasu bayan cece-kuce da suka jawo sosai.

Shuwagabannin majalisar tarayya da shuwagabannin kungiyoyin gwamnoni da ministan kudi da sauran manyan ma’aikatan Gwamnati ne zasu shaida wannan lamari a fadar shugaban kasar kamar yanda sanarwar ta tabbatar.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Miji ya kai matarsa kara ofishin 'Yansanda inda yace yana zargin ta ci amanarsa saboda ta haifa masa farar diya bayan shi da matar tasa duk bakakene

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *