Thursday, February 5
Shadow

Abin takaici wasu daliban mata har dan kamfai dinsu nake hangowa saboda shigar banza>>Malamin Jami’a ya koka

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Wani malamin jami’a ya koka da cewa, shigar banza ta yi yawa tsakanin dalibai mata.

Malamin me suna Mr Ishaq Ibrahim na koyarwa ne a jami’ar University of Professional Studies, Accra (UPSA) ta kasar Ghana.

Yayi wannan korafine a yayin hira dashi a gidan talabijin na Metro TV ranar Alhamis, July 3, 2025.

Malamin yace ya kamata a dauki matakin gyara dan kare martabar jami’ar ta UPSA.

Yace akwai sanda yake koyar da dalibai wata daliba data zauna a gabansa saboda gajartar siket din data saka, har dan kamfai dinta yana hangowa.

Yace abin yayi muni a lokacin da cutar Corona Virus ta zo inda yace saboda a kwamfuta ake karatu kuma kowa zai iya shiga aji ta hanyar kiran waya da bidiyo call.

Karanta Wannan  Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un: Kalli Bidiyon yanda aka kama wata Yarinya da aka tura Islamiya a Otal

Yace wata dalibar da kayan bacci take shiga ajin, wata kuma ban daki zata shiga tana wanka tana sauraren karatun.

Da yawa dai sun yi kiran a dauki matakin gyara kan lamarin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *