Thursday, February 26
Shadow

Akwai yiyuwar Tinubu ba zai so sauka daga Mulki ba, zai so ci gaba da zama shugaban Najeriya har karshen rayuwarsa>>Inji El-Rufai

Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yi gargadi cewa muddin ‘yan Najeriya basu tashi tsaye ba suka yi abinda ya kamata a 2027 ba, to lallai Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai so ya zarce ya mulki Najeriya har iya tsawon rayuwarsa.

El-Rufai ya kwatanta Abinda Tinubu ke son yi da irin mulkin shugaban kasar Kamaru, Paul Biya.

El-Rufai yayi wannan maganane a yayin da Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya kai masa ziyarar jaje bayan tarwatsa taron ADC da aka yi a Kaduna.

El-Rufai yace ko mulkin Soja bai ga ana yin irin kamar karyar da Gwamnatin Tinubu ke yi ba

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Mijina bai iya soyayya ba, ko Kis bai taba min ba tunda muka yi aure, kullun kawai saidai ya zo yace in bude mai>>Matar aure ta kaiwa Fasto karar Mijinta

Dan haka yace dolene a hada kai.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *