Wednesday, March 25
Shadow

An kama Alkali da zargin satar kudi a asusun me laifi da aka kai kotu ake tuhumarsa a Kano

Hukumar kula da Shari’a ta Kano ta hukunta wasu alkalai a jihar saboda aikata ba daidai ba.

Alkalai uku ne dai da maga takarda a babban kotun jihar aka hukunta ciki hadda alkalin da yayi yunkurin satar kudi daga asusun wanda ake tuhuma.

Kakakin hukumar Baba Jibo-Ibrahim ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar.

Yace wadanda ake zargin sune Magistrate Rabi Abdulkadir, Magistrate Talatu Makama, da Magistrate Tijjani Saleh-Minjibir.

Sanarwar tace an dauki matakin ladabtarwar ne dan tsaftace bangaren shari’a na jihar.

Karanta Wannan  Mai martaba Sarkin Kano Alh Aminu Ado Bayero ya karbi bakuncin yan Majalisar dokoki na Jahar kano tsagin jam’iyyar APC, sun kawo ziyara tare da jaddada mubayi’ar su

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *