Thursday, February 5
Shadow

An kama wani dalibi a jihar Naija saboda zargin sukar Gwamnan Jihar

Rahotanni daga jihar Naija na cewa, an kama wani dalibin jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida University saboda zargin ya soki gwamnan jihar, Mohammed Umar Bago.

Sunan dalibin da aka kama Abubakar Isah Mokwa kuma an kamashine ranar Alhamis a dakinsa dake garin Lapai.

An kamashine bayan da yayi rubutu yana sukar Gwamnan Gwamnan a shafinsa na Facebook.

Kakakin ‘yansandan jihar, SP Wasiu Abiodun ya tabbatar da kamen inda yace suna kan binciken wanda akw zargin.

Karanta Wannan  Zaku yi Azumi cikin Mutunci da jin dadi saboda zamu tabbatar an samu tsayayyar wutar Lantarki>>Gwamnatin Tarayya ta baiwa Musulmai tabbaci

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *