Friday, December 5
Shadow

An rushe sabon Ofishin yakin neman zaben shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da aka gina a jihar Benue

Rahotanni daga jihar Benue na cewa, an rushe sabon ofishin yakin neman zaben shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da aka gina a jihar.

Ranar Alhamis ne Hukumar kula da raya birane ta jihar Benue din ta rushe wannan gini wanda kuma shine Hedikwatar yakin neman zaben Tinubu a jihar.

Sati daya kenan da bude wannan ofishin.

Shugaban kungiyar magoya bayan Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a jihar Tarnongo Simon yayi Allah wadai da lamarin inda yace sun cika duka sharudan mallaka da ginin wannan ofishi nasu kamin a rusheshi.

Karanta Wannan  Wata Sabuwa: Gwamnatin tarayya ta cire Tallafin CNG wanda a baya ta kawo tace shine zai maye man fetur ta fara bayar da tallafi a kanshi, Kuma har farashin ya tashi sosai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *