
Jama’a na ta kira a kama Tubabben tsageran Niger Delta, Tampolo bayan ganinsa yana wulakanta takardar Naira.
Da yawa sun kira EFCC ta kama Tampolo ta hukuntashi indai ba talakawa kadai ake hukuntawa ba idan sun wulakanta takardar Nairar.
A baya dai EFCC ta kama mutane irin su Murja Kunya, Bobrisky da sauransu inda ake zarginsu da wulakanta Naira.