Friday, December 19
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Da Duminsa: A karin farko, Musulma me sanye da Hijabi, Ameera Hashwi, ta zama Sarauniyar kyau a kasar Amurka

Da Duminsa: A karin farko, Musulma me sanye da Hijabi, Ameera Hashwi, ta zama Sarauniyar kyau a kasar Amurka

Duk Labarai
Matashiya, Ameera Hashwi me shekaru 25 ta zama Sarauniyar kyau ta garin Wayne County, Michigan kasar Amurka. Ta kafa tarihi inda ta zama ta farko, Musulma kuma me sanye da hijabi da ta kafa wannan Tarihi. Ta kammala karatu daga jami'ar Dearborn Heights inda ta karanci Lauya. Saidai hakan ya tayarwa Amurkawa fararen fata hankali sosai inda suke tambayar ya akai aka bari haka ya faru?
Shugaba Tinubu ya bar Abuja dan ziyara zuwa kasashen Japan da Brazil

Shugaba Tinubu ya bar Abuja dan ziyara zuwa kasashen Japan da Brazil

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bar Abuja a yau, Juma'a dan zuwa kasashen Japan da Brazil ziyara. Shugaban zai tsaya a Dubai, UAE kamin ya ci gaba da tafiyar tasa. Shugaba Tinubu ya tashi daga filin jirgin Nnamdi Azikiwe da misalin karfe 11:15 na safiyar yau. Manyan jami'an gwamnati da suka hada da shugaban ma'aikatan fadar Gwamnati, Femi Gbajabiamila, da babban me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu, da Ministan kudi, Wale Edun sun halarci filin jirgin.
Kungiyar malaman kwalejojin Kimiyya da fasaha, ASUP sun baiwa Gwamnatin Tarayya wa’adin akwanaki 21 a biya musu bukatunsu ko su tafi yajin aiki

Kungiyar malaman kwalejojin Kimiyya da fasaha, ASUP sun baiwa Gwamnatin Tarayya wa’adin akwanaki 21 a biya musu bukatunsu ko su tafi yajin aiki

Duk Labarai
Kungiyar malaman Kwalejojin Ilimin Kimiyya da Fasaha ASUP ta baiwa gwamnatin tarayya wa'adin kwanaki 21 a biya musu bukatunsu ko su tafi yajin aiki. Shugaban kungiyar, Comrade Shammah Kpanja ya bayyana hakan ga manema labarai a Abuja ranar Juma'a. Yace daya daga cikin abubuwan da suke bukata shine a kafa hukuma me kula da ayyukan kwalejojin Ilimin kimiyya da fasaha. Sannan kuma ya kara da cewa auna neman a daidaita sakamakon kammaga kwalejojin ilimin kimiyya na HND da Kwalin Digiri da ake bayarwa bayan kammala Jami'o'i.
Kalli Bidiyo: Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya ce ba ya son a yafe masa zunubansa dan haka ba zai koma jam’iyyar APC ba

Kalli Bidiyo: Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya ce ba ya son a yafe masa zunubansa dan haka ba zai koma jam’iyyar APC ba

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya bayyana cewa ba zai koma jam'iyyar APC ba kawai dan a yafe masa zunibansa. Tambuwal ya bayyana hakane a bayan da ya fito daga ofishin EFCC bayan kamun da suka masa. An kama Tambuwal bisa zargin cewa, ya cire Naira Biliyan 189 daga asusun bankin ajiyar jihar. https://twitter.com/jrnaib2/status/1956262313893253412?t=gWOOELY_ZAWEIw9kGNJYdA&s=19
Gwamna Dikko Raɗɗa zai fara biyan Limaman Coci alawus-alawus, zai ɗauki Malaman da za su karantar da addinin kiristanci a Katsina

Gwamna Dikko Raɗɗa zai fara biyan Limaman Coci alawus-alawus, zai ɗauki Malaman da za su karantar da addinin kiristanci a Katsina

Duk Labarai
Gwamna Dikko Raɗɗa zai fara biyan Limaman Coci alawus-alawus, zai ɗauki Malaman da za su karantar da addinin kiristanci a Katsina. Gwamnatin Jihar Katsina ta amince da bayar da alawus-alawus ga Limaman Coci a matsayin wani ƙoƙari na haɗin kai a addinai da kuma bayar da gudummawa ga Malaman addinai. Ƙungiyar Kiristoci ta kasa reshen jihar Katsina ta sanar da hakan a cikin wata sanarwa da sakataren Kungiyar Dakta Musa Daniel Danladi ya fitar a madadin Shugaban Ƙungiyar Very Rev. Fr. Richard Shuaibu Liti. Haka zalika, yace Gwamna Dikko Umaru Raɗɗa ya amince da ɗaukar Malaman da suka karanci addinin kiristanci domin karantarwa a makarantun gwamnati, inda Kungiyar CAN ta bayyana cewa hakan zai tabbatar da daidaito da ci gaba, tana mai cewa ƙungiyar ta daɗe tana neman haka. Usman...
Kalli Bidiyo: Yanda mutane suka rikawa motocin ‘yan siyasa rotse da duwatsu a Zaria, Kaduna

Kalli Bidiyo: Yanda mutane suka rikawa motocin ‘yan siyasa rotse da duwatsu a Zaria, Kaduna

Duk Labarai
An ga Bidiyon yanda aka rikawa motocin 'yan siyasa rotse a Zaria jihar Kaduna. An ji matasa na fadin bama so, bamayi. Saidai kowane bangare tsakanin APC da ADC na ikirarin cewa abokan hamayarsa ne akawa hakan, wasu na cewa 'yan APC ne akawa haka yayin da wasu ke cewa 'yan ADC ne akewa hakan. A ranar Asabar ne dai za'a gudanar da zabe a wasu bangarori na jihar. https://twitter.com/Abdullahigoslow/status/1956099059267027228?t=SWVNuTEqjxCd79sLJH6lng&s=19 Akwai adawa me zafi tsakanin Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad da Gwamna me ci, Malam Uba Sani.
Kalli Bidiyo: Inda Gwamna Abba Kabir Yusuf yace yana bayar da Naira Dubu 50 a rika baiwa matasa duk wata a wajan wani taro da ya halarta, saidai matasan sun ce ba’a basu ko sisi

Kalli Bidiyo: Inda Gwamna Abba Kabir Yusuf yace yana bayar da Naira Dubu 50 a rika baiwa matasa duk wata a wajan wani taro da ya halarta, saidai matasan sun ce ba’a basu ko sisi

Duk Labarai
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa daya daga cikin ayyukan da yakewa jihar Kano Shine baiwa matasa tallafin Naira dubu 50 a wata. Ya bayyana hakane a wajan wani taron siyasa. Saidai matasan sun musanta wannan ikirari na gwamnan inda suka ce ba'a basu ko sisi. Gwamnan dai yace zai yi bincike kan lamarin.
Matsalar tsaro ta janyowa Najeriya asarar Naira Tiriliyan 7.17 sannan kaso 40 na dabbobin da ake dasu sun salwanta saboda matsalar

Matsalar tsaro ta janyowa Najeriya asarar Naira Tiriliyan 7.17 sannan kaso 40 na dabbobin da ake dasu sun salwanta saboda matsalar

Duk Labarai
Wata Kungiya me sun, Agramondis Research and Consulting ta bayyana cewa matsalar Tsaro ta jawowa Najeriya asarar Naira Tiriliyan 7.17 sannan kaso 40 cikin 100 na dabbobin da ake dasu sun salwanta. Rahoton yace bangaren dabbobi na taimakawa da kaso 10 cikin 100 na ci gaban Najeriya sannan ya samarwa mutane Miliyan 4.5 aikin yi amma gwamnati bata zuba jari sosai a bangaren. Kungiyar tace fari, Canjin Yanayi da matsalar tsaro, da karancin ruwan sama da rikicin manoma da makiyaya na kawowa bangaren tsaikon ci gaba. Dan hakane ta yi kira ga gwamnatin tarayya ta kawo dauki a hangaren ta hanyar ilimantar da manoma da makiyaya da basu tallafi da kayan aiki na zamani
Gwamna Abba Kabir Ya Baiwa Matashin Yaro Mai Harkar Kere-Kere A Kano Jari Na Makuden Kudade Tare Da Daukar Nauyin Karatunsa

Gwamna Abba Kabir Ya Baiwa Matashin Yaro Mai Harkar Kere-Kere A Kano Jari Na Makuden Kudade Tare Da Daukar Nauyin Karatunsa

Duk Labarai
Gwamna Abba Kabir Ya Baiwa Matashin Yaro Mai Harkar Kere-Kere A Kano Jari Na Makuden Kudade Tare Da Daukar Nauyin Karatunsa. {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Hazikin matashin nan mai harkar kere-kere, Injiniya Khalifa, ya samu tallafin makuden kudade daga wurin Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf domin ci gaba da harkar kere-kerensa kamar yadda ya jima yana ta neman jari. Haka kuma Gwamna zai dauki nauyin ci gaba da karatunsa. Daga Fauziyya D. Sulaiman