Sunday, May 25
Shadow

Author: Auwal Abubakar

Kada wanda ya kara kiran shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da su an banza na T-Pain>>Fadar shugaban kasa ta yi gargadi

Kada wanda ya kara kiran shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da su an banza na T-Pain>>Fadar shugaban kasa ta yi gargadi

labaran tinubu ayau
Fadar shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu ta yi gargadin kada wanda ya kara kiran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da sunan banza na T-Pain. Sunan T-Pain dai a kafar sada zumunta aka sakawa shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu shi dan nuna wahalar da mutane ke ciki a karkashin Gwamnatinsa wanda sunan wani mawakin kasar Amurka ne. Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar na daga cikin wadanda suka rika kiran Tinubu da wannan suna. Saidai duk da gargadin da fadar shugaban kasar ta yi,da yawa sun ce ba zasu daina fadar wannan suna ba.
Wata Sabuwa: Gwamnati ta saka haraji akan gawarwaki a Najeriya

Wata Sabuwa: Gwamnati ta saka haraji akan gawarwaki a Najeriya

Duk Labarai
Gwamnatin jihar Enugu ta sanar da saka haraji akan gawarwakin da aka ajiye a mutuwaren dake Asibitocin jihar. Saidai gwamnatin tace ba da niyyar tatsar mutane da tara kudade barkatai bane ta aikata hakan. Shugaban hukumar tara kudaden shiga na jihar, Mr Emmanuel Nnamani Ya yi karin haske kan lamarin inda yace duk gawar da aka kai mutuware a jihar kuma 'yan uwanta basu dauketa ba har ta wuce awanni 24 watau kwana daya to duk rana za'a rika biya mata harajin Naira 40 har zuwa ranar da za'a dauketa daga mutuwaren. Yace wannan ba sabuwar haraji bace kuma an dauki matakinne dan hana mutane kai gawarwakinsu mutuware a jihar.
Ji abinda Sanata Shehu Sani ya cewa matar tsohon gwamnan Kaduna, Hadiza El-Rufai bayan da ta masa gyaran kuskuren turancin da yayi

Ji abinda Sanata Shehu Sani ya cewa matar tsohon gwamnan Kaduna, Hadiza El-Rufai bayan da ta masa gyaran kuskuren turancin da yayi

Duk Labarai
{"remix_data":[],"source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Matar tsohon gwamnan jihar Kaduna, Hadiza El-Rufai ta yiwa sanata Sanata Shehu Sani gyaran kuskuren Turancin da yayi a shafinsa na Twitter. Saidai da alama Sanata Sani bai ji dadin wannan gyara da ta masa ba inda mata martani da cewa, mun daina bibiyar juna a kafafen sada zumunta dan Allah ki kyaleni. https://twitter.com/ShehuSani/status/1845415955582640232?t=pDi22Zq04krnhwf4X1a_ew&s=19 Lamarin dai ya dauki hankula sosai inda wasu ke cewa ya kamata ya karbi gyaran da aka masa wasu kuma na goyon bayansh...
Me neman kafa kasar Yarbawa ta Oduduwa, Sunday Igboho ya kaiwa kasar Ingila bukatar ta goyi bayan kafa kasar Yarbawan

Me neman kafa kasar Yarbawa ta Oduduwa, Sunday Igboho ya kaiwa kasar Ingila bukatar ta goyi bayan kafa kasar Yarbawan

Duk Labarai
Me fafutukar kafa kasar Oduduwa, Sunday Igboho ya kai takardar neman goyon bayan kafa kasar Yarbawan zuwa ga ofishin kasar Ingila dake Landan. Sunday Igboho yayi kokarin ganin kafa kasar ta Oduduwa amma bai cimma nasara ba inda a karshe sai da ya tsere daga Najeriya saboda yanda jami'an tsaro ke nemansa ruwa a jallo.
Kasar Namibia ta nemi Najeriya ta taimaka mata yin yaki da cin hanci

Kasar Namibia ta nemi Najeriya ta taimaka mata yin yaki da cin hanci

Duk Labarai
A kokarinta na yaki da rashawa da cin Hanci, Kasar Namibia ta nemi taimakon Najeriya wajan yaki da cin hanci inda tace tana neman shawarar Najeriyar ne saboda yanda kasar ke da kwarewa a fannin. Kasar ta Namibia ta samu ci gaba sosai saidai tana fama da matsalar rashawa da cin hanci wanda hakan yasa mutane basu da yadda da gwamnatin tasu. Kallon Nasarar da hukumomin yaki da rashawa da cin hanci na EFCC da ICPC ke samu yasa kasar ta Namibia ta nemi taimakon Najeriya wajan yaki da rashawa a kasarta. Kasar tana neman Najeriya ta taimaka mata wajan kafa nata hukukomin na yaki da rashawa da cin hanci.

Yadda ake dafa taliya

Abinci
Taliya na da saukin Dafawa kuma ana hadata da abubuwa daban-daban wajan ci, irin su wake, shinkafa, Makaroni da sauransu. Idan Taliya za'a dafa wadda babu komai a cikinta watau fara ba dafa duka ba. Kawai ruwa za'a saka babban Kofi uku a tukunya a barshi ya tafasa, sai a saka taliya leda daya a ciki. A barta ta dahu amma kada ta wuce minti 10 zuwa 15 sai a sauke, idan akwai sauran ruwa a tace idan kuma babu sai aci da abinda ake so watau Miya ko wani abu daban.

Ya ake gane cikin mace

Haihuwa, Laulayin ciki
Idan ciki ya kai sati 20, gwajin Ultrasound yakan iya nuna cikin macene ake dauke dashi ko Namiji. Hakanan akwai gwajin Amniocentesis da shima ake yi wanda ke nuna jinsin jaririn da ake dauke dashi. Bayannan akwai alamu na gargajiya da ake amfani dasu wajan ganewa ko hasashen cikin mace. Ciki Yayi sama: Wasu na cewa idan ciki yayi sama sosai, to wannan alamace dake nuna cewa diya macece za'a haifa. Girman Nono: Hakanan akwai bayanan dake cewa idan nonon mace na hagu yafi na dama girma shima alamace dake nuna mace za'a haifa ba Namiji ba. Ciwon Safe: Ciwon safe na daya daga cikin dalilan da ake alakanta cikin diya mace dashi inda me ciki zata rika jin kamar zata yi amai, kasala da sauransu. Kalar Fitsari: Hakanan akwai bayanan dake nuna cewa kalar fitsarin mace ya zama kal...
Kalli Bidiyon wasu na rokon Kabarin Shehu ya kawowa Najeriya saukin tsadar man fetur ya dauki hankula

Kalli Bidiyon wasu na rokon Kabarin Shehu ya kawowa Najeriya saukin tsadar man fetur ya dauki hankula

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wasu mutane da suka kaiwa shehunsu ziyara sun rika rokonsa akan ya kawowa Najeriya saukin tsadar man fetur da ake ciki. An ji suna gayawa shehun cewa, tsadar man fetur din ta hana ziyara. https://www.tiktok.com/@user2139247130913/video/7424490101805288710?_t=8qUdKfQU7O9&_r=1 Lamarin dai ya jawo cece-kuce sosai a shafukan sada zumunta inda wasu ke kafurtasu wasu kuma na karesu.
Kalli Bidiyo: Me barkwanci na Kudu, Sabinus yayi wasa da addinin Musulunci kuma musulmai sun nuna masa fushinsu

Kalli Bidiyo: Me barkwanci na Kudu, Sabinus yayi wasa da addinin Musulunci kuma musulmai sun nuna masa fushinsu

Duk Labarai
Tauraron me barkwanci na kudu, Sabinus ya yi barkwanci da addinin Musulunci saidai musulmai da yawa aun gargadeshi. Yayi bidiyonne inda ya yi Atishawa sai wasu muryoyi ke ta magana a baya. https://www.tiktok.com/@sabinus1_/video/7400424002625211654?_t=8qUVFW0FfN8&_r=1 Da yawa dai sun bayyana masa cewa a addinin musulunci ba'a wasa da ibada.
Labari Me Dadi: Saboda karin kudin man fetur da NNPCL ta yi, Kungiyar ‘yan kasuwar man fetur ta IPMAN tace zata shigo da mai me arha daga kasashen waje

Labari Me Dadi: Saboda karin kudin man fetur da NNPCL ta yi, Kungiyar ‘yan kasuwar man fetur ta IPMAN tace zata shigo da mai me arha daga kasashen waje

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Kungiyar dillalan man fetur ta IPMAN ta bayyana cewa, zata fara nemo man fetur me arha ko da daga kasashen wajene. Ta bayyana hakane ta bakin kakakinta, Chief Chinedu Ukadike a hirarsa da jaridar Vanguard. Yace a yanzu tunda NNPCL ba su ne kadai masu shigo da man fetur ba, zasu iya shigo da man fetur dinsu daga duk inda suke so. Hakan na zuwane bayan da kamfanin na man fetur na kasa, NNPCL ya kara farashin man fetur din zuwa Naira 998 a wasu guraren kuma Naira 1030 akan...