Monday, March 30
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Saudiyya ta tanadi jami’an tsaro 40,000 domin Hajjin bana

Saudiyya ta tanadi jami’an tsaro 40,000 domin Hajjin bana

Duk Labarai
Saudiyya ta tura sama da jami’an tsaro 40,000 don tabbatar da tsaro yayin aikin hajjin 2025. Da yake jawabi a wani bikin gagarumin faretin soji da aka gudanar a birnin Makkah, Mohammad bin Abdullah Al-Bassami, darektan tsaron jama'a kuma shugaban kwamitin tsaron hajji, ya ce dukkan sassan tsaro an tura su domin aiwatar da shirin tsaro na bana, tare da karin bayani cewa jami’an tsaron suna cikin shirin ko-ta-kwana kuma a shirye suke su dauki matakin gaggawa idan ya taso. “An tanadi dukkan abinda ake bukata domin tabbatar da tsaron lafiyar mahajjata da jin dadinsu a lokacin aikin hajji,” in ji shi. “Jami’an tsaronmu suna cikin matakin shiri mafi girma don fuskantar kowanne hali da zai iya barazana ga tsarkin wannan ibada. “Muna da kwarin guiwar tabbatar da cewa mahajjata za su gu...
Mahaifiyar dalibi me rubuta jarabawar WAEC ta dauko hayar ‘yan Iska sun zane malamin danta saboda ya hana dan nata satar Jarabawa

Mahaifiyar dalibi me rubuta jarabawar WAEC ta dauko hayar ‘yan Iska sun zane malamin danta saboda ya hana dan nata satar Jarabawa

Duk Labarai
Wani malami a makarantar Complete Child Development College Aule dake Akure jihar Ondo ya sha duka bayan da ya hana daya daga cikin dalibansa satar jarabawa a yayin da ake rubuta jarabawar WAEC. Ana zargin mahaifiyar dalibinne ta dauki hayar 'yan Iska suka zane malamin Dama dai malamin da farko ya hana dalibin satar jarabawa saidai dalibin yaki dainawa inda ya gayawa mahaifiyarsa. Mahaifiyarsa ta je makarantar inda ta yi barazanar yin maganin duk wanda ya sake ya hana danta satar Jarabawa. Saidai malamin me suna Rotifa wanda shine mataimakin shugaban makarantar ya sha alwashin sai ya hana dalibin satar jarabawar duk da barazanar mahaifiyarsa. Hakan kuwa aka yi da dalibin ya koma makarantar sai ya je da waya ya fiddo zai yi satar Amsa amma malamin ya kwace wayar. Nan ne ma...
Shugaban kasar Nijar ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da kasarsa

Shugaban kasar Nijar ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da kasarsa

Duk Labarai
Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya da haɗa baki da Faransa da China da Amurka wajen ɗaukar nauyin ayyukan ta’addanci a ƙasarsa. A cikin wani jawabi na awa uku da aka watsa kai tsaye a gidan talabijin na Radio-Télévision du Niger (RTN) a ƙarshen mako, Tchiani ya yi magana da harshen Hausa, Zabarma da Faransanci, inda ya zargi Najeriya da Jamhuriyar Benin da Faransa da China da Aljeriya da Amurka da kokarin dagula ko cutar Nijar da sauran ƙasashen da ke cikin ƙawancen AES. Wannan shi ne karo na biyu da Tchiani ke zargin Najeriya a yayin wata hira da ya yi ta ranar Kirsimeti a bara, inda ya ce Faransa na haɗa baki da ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya a yankin tafkin Chadi domin lalata tsaron Nijar, tare da sanin Najeriya. Tchiani ya ƙara da cewa an ...
Dakarun sojin ruwa na Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa>>Inji Shugaban Sojojin

Dakarun sojin ruwa na Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa>>Inji Shugaban Sojojin

Duk Labarai
Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa sun yi kaɗan wajen tabbatar da tsaron gaɓar ruwan ƙasar da kuma daƙile satar man fetur. Da yake magana ta kafar talabijin ta Channels TV a yau Litinin, Vice Admiral Emmanuel Ogalla ya ce jimillar dakarun rundunar tasa ba su 30,000 da ɗoriya ba. Sai dai ya ƙara da cewa mahukunta sun ƙara yawan adadin mutanen da suke ɗauka duk shekara domin cike giɓin. "Za ku sha mamaki idan kuka ji cewa dakarun rundunar sojin ruwa ba su wuce 30,000 da ɗoriya ba," in ji shi. "Amma kuma muna da gaɓar ruwa mai girman kashi ɗaya cikin uku na faɗin ƙasar Najeriya baki ɗaya. Muhimmin abu dai shi ne muna ƙoƙarin ƙara yawan dakarun."
Gwamnatin tarayya ta ayyana ranakun Juma’a 6, da Litinin 9 ga watan Yuni, 2025 a matsayin ranakun hutu domin gudanar da bukukuwan babbar Sallah na bana

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranakun Juma’a 6, da Litinin 9 ga watan Yuni, 2025 a matsayin ranakun hutu domin gudanar da bukukuwan babbar Sallah na bana

Duk Labarai
Ministan harkokin cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, wanda ya bayyana hakan a madadin gwamnatin tarayya, ya taya daukacin al’ummar musulmi na gida da kuma na kasashen waje murnar sallah. Ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su ci gaba da yin koyi da sadaukarwa da imani da kuma amfani da wannan lokacin wajen yi wa Nijeriya addu’a ta zaman lafiya da kwanciyar hankali. Ministan ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa gyare-gyare da tsare-tsare da suka shafi jama’a da aka yi, a ci gaban ajandar sabunta fata na gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, shi ne dawo da Nijeriya kan turbar ci gaba. Yayin da yake yiwa al'ummar musulmi barka da Sallah, Ministan ya bukaci dukkan 'yan Najeriya da su hada kai da gwamnati mai ci a kokarinta na dawo da martabar Najeriya a matsayin kasa mai girma.
Sunan Muhammad ya shiga cikin sunaye mafiya shahara a kasashen Turai da ake sakawa Jarirai

Sunan Muhammad ya shiga cikin sunaye mafiya shahara a kasashen Turai da ake sakawa Jarirai

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, sunan Muhammad ya shiga cikin jerin sunaye mafiya shahara a kasar Ingila inda aka sakawa jarirai 4,661 sunan. A Brussels kuwa sunan Mohamed shine yazo na daya. Hakanan a Jamus ma sunan Muhammad ya shahara sosai. A Netherlands kuwa sunan Muhammad shine ya zo na 2. A Norway kuwa sunan Mohammed na daya yazo. A Ireland ma sunan Muhammad ya taba zuwa na daya a shekarar 2022.
Bama sacewa ko yin Almubazzaranci da kudin da muka ciyo bashi, ayyukan gina kasa muke yi dasu>>Inji Shugaba Tinubu

Bama sacewa ko yin Almubazzaranci da kudin da muka ciyo bashi, ayyukan gina kasa muke yi dasu>>Inji Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, basa sacewa ko yin Almubazzaranci da kudaden da aka ciwo bashi. Shugaban ya bayyana hakanne a ta bakin kakakinsa, Bayo Onanuga. Inda ya kara da cewa, kudaden da suke ciwo bashi ya zama dole saboda mafi yawanci ayyukan titi da sauran wasu basa cikin kasafin kudi, yace dan haka dole a ciwo bashi. Yace kuma ba Najeriya ce kadai kasar dake ciwo bashi ba, hatta kasashe manya irin su Amurka na ciwo bashi.
Kalli Bidiyon:Yanda Kishin Addinin Musulunci ya sa shahararren dan danbe, Khabib Nurmagomedov yaki gaisawa da mace ‘yar Jarida

Kalli Bidiyon:Yanda Kishin Addinin Musulunci ya sa shahararren dan danbe, Khabib Nurmagomedov yaki gaisawa da mace ‘yar Jarida

Duk Labarai
Shahararren dan Dambe daga kasar Rasha, Khabib Nurmagomedov yaki yadda ya gaisa da mace 'yar jarida bayan data bashi hannu. Lamarin ya farune bayan kammala wasan gasar cin kofin Championships League wanda kungiyar PSG ta lashe. https://twitter.com/AzatAlsalim/status/1929216302746378627?t=_R7lM6v3JBYTXlUgGt-FSA&s=19 Khabib Nurmagomedov ya gaisa da 'yan uwansa maza inda itama 'yar jaridar ta mika masa hannu su gaisa, amma yaki yadda ya bata hannu, daga baya dai ta bashi hakuri. Ya sha Yabo kan lamarin.
Kuma Dai: Jirgin Yakin Sojin Najeriya ya Kàshè ‘yan Bijilante bisa kuskure a jihar Zamfara

Kuma Dai: Jirgin Yakin Sojin Najeriya ya Kàshè ‘yan Bijilante bisa kuskure a jihar Zamfara

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Zamfara na cewa, jirgin yakin sojin Najeriya ya kashe 'yan Bijilante bisa kuskure a jihar Zamfara. Shafin Bakatsina ya ruwaito cewa, lamarin ya farune a kauyen Mani dake kamar Hukumar Maru dake jihar. Yace an kashe manoma 50 da yin garkuwa da mutane 20 a ranar da lamarin ya faru bayan harin 'yan Bindiga. Yace jirgin da aka kawo dan ya taimaka a yi maganin 'yan Bindigar sai ya kare da kashe 'yan Banga bisa kuskure. Zuwa yanzu dai Gwamnatin jihar Zamfara da Hukumomin tsaro basu ce uffan ba kan lamarin.
Ka rage yawan cin Bashi>>IMF ta gargadi shugaba Tinubu

Ka rage yawan cin Bashi>>IMF ta gargadi shugaba Tinubu

Duk Labarai
Kungiyar bayar da lamuni ta Duniya, IMF ta gargadi Najeriya kan ci gaba da ciwo bashi duk da yanda tattalin arzikin kasar ya tabarbare. Hakan na zuwane yayin da Gwamnatin Bola Ahmad Tinubu ke shirin cin bashin da ya kai kusan Dala Biliyan $26. Kungiyar tace kusan kaso 60 na kasafin kudi da gwanatin Tinubu ke dashi da bashi take kokarin aiwatar dashi inda tace hakan ya sabawa Alkawarin Gwamnatin Tinubu din na kaucewa bashi da mayar da hankali wajan jawo masu zuba hannun jari a Najeriya. Kungiyar tace karuwar bashin Najeriya abu ne me hadarin gaske. Sannan tace tana bayar da shawarar a mayar da hankali wajan samun kudi ta cikin gida da fadada hanyoyin kudin shigar Gwamnati ya fi a mayar da hankali wajan yawaita ciwo bashi. Kungiyar tace duk da yawaitar bashin da Najeriya ke c...