YANZU-YANZU: Kakakin Majalisa Tajudeen Abbas Ya Janye Kudirin Tilasta Zaɓe wanda za’a rika cin mutum tarar Naira dubu dari bayan da ya sha suka
Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Tajudeen Abbas, ya janye kudirin dokar da ke neman tilasta wa 'yan Najeriya kada kuri'a a kowane zaɓe.
Kudirin dai na neman gyara Dokar Zaɓe ta 2022, inda aka tanadi cewa duk masu cancantar kada kuri’a dole ne su fito su zaɓa a kowanne zabe, kuma wanda ya ki, zai iya fuskantar hukunci na daurin watanni shida zuwa tara, ko tara har Naira 100,000.
Sai dai, wannan kudiri ya jawo ce-ce-ku-ce daga jama’a da kungiyoyin kare hakkin dan adam. Kungiyar SERAP ta bayyana cewa wannan yunkuri ya sabawa yancin dan adam, kundin tsarin mulki da kuma dokokin kasa da kasa. Sun jaddada cewa 'yancin kada kuri’a yana nufin mutum na da damar yanke shawara – ya kada kuri’a ko kuma ya ki. Haka kuma, sun yi barazanar daukar matakin shari’a idan aka amince da kudirin.
Fi...








