Friday, March 20
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Mun kusa ƙaddamar da haɗakar kawar da APC – Ƴan adawa

Mun kusa ƙaddamar da haɗakar kawar da APC – Ƴan adawa

Duk Labarai
Manyan ƴan siyasar Najeriya da ke jagorantar shirin yin haɗaka tsakanin jam'iyyun hamayya domin tunkarar APC a zaɓen 2027, sun mayarwa ƙungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP martani, a kan matsayar da gwamnonin suka ɗauka cewa ba su goyon bayan ƙulla duk wata haɗaka da za ta fitar da su daga PDP. Gamayyar ƴan adawar da ta haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar Labour a zaɓen 2023 da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai da dai sauran ƴan siyasa, ta ce nan ba da jimawa ba za a sanar da ƙulla sabuwar haɗakar siyasa da za ta ceto Najeriya daga mulkin APC. Ɗaya daga cikin jagororin tafiyar ƙulla sabuwar haɗakar siyasar ta Najeriya kuma tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar APC na ƙasa mai kula da shiyyar Arewa Maso Yamma, Sali...
‎Hukumar tace fina-finai ta Kano ta fara kamen Baburan Adai-daitasahu masu ɗauke da hotuna da rubuce-rubuce na rashin ɗa’a

‎Hukumar tace fina-finai ta Kano ta fara kamen Baburan Adai-daitasahu masu ɗauke da hotuna da rubuce-rubuce na rashin ɗa’a

Duk Labarai
‎‎‎‎Hukumar Tace Fina-finai da Dab’i ta Jihar Kano ta kaddamar da wani sabon atisayen kama baburan adai-daita sahu da ke dauke da hotunan batsa da rubuce-rubuce marasa tarbiyya a manyan titunan jihar.‎‎Shugaban hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha, ne ya tura jami’an sa don gudanar da wannan aiki, inda ya bayyana cewa hakan na daga cikin nauyin da ke kan hukumar na tabbatar da tsaftar hotuna da rubuce-rubuce da ke bayyana a fili ga al’umma.‎‎Sanarwar ta fito ne daga Abdullahi Sani Sulaiman, Jami’in Hulda da Jama’a na Hukumar Tace Fina-finai da Dab’i ta Jihar Kano.‎‎‎“Aikinmu shi ne tabbatar da cewa babu wani hoto ko rubutu da zai cutar da tarbiyya ko dabi’un al’umma, musamman matasa, ya fito fili ba tare da tantancewa ba,” in ji Abba El-Mustapha.‎‎‎Daraktan Sashen Dab’i na hukumar, Alhaji Abub...
Wani matashi da ya kàshè mutane wajen ƙwacen waya ya kai kan sa wajen ƴansanda a Kano

Wani matashi da ya kàshè mutane wajen ƙwacen waya ya kai kan sa wajen ƴansanda a Kano

Duk Labarai
Wani matashi mai shekaru 20 da ya amsa da bakin da cewa ya kashe mutane wajen ƙwacen waya a gurare daban-daban ya miƙa kansa da kansa ga rundunar ‘yansanda ta jihar Kano. Wanda ake zargin, wanda aka bayyana sunansa da Umar Auwal, mai lakabi da ‘Abba Dujal,’ mazaunin karamar hukumar Wudil a jihar Kano, ya amsa cewa yana da hannu a laifukan kisan kai, fashi da makami da kuma sata, musamman na babura da wayoyin hannu. Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano, SP Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa miƙa kansa da Auwal ya yi ya biyo bayan zurfafa samame da rundunar ke yi a maboyar ‘yan ta’adda a jihar. Kiyawa ya ce wannan mataki yana daga cikin kokarin da rundunar ke yi na dawo da doka da oda da kuma kare rayuka da dukiyoyin al’umma. Auwal ya amsa cewa ya daba wa wani...
Da Duminsa: Dangote ya sake rage farashin Man fetur dinsa

Da Duminsa: Dangote ya sake rage farashin Man fetur dinsa

Duk Labarai
Matatar Man fetur ta Dangote ta sake sanar da kara rage farashin Man fetur dinta inda a yanzu take sayarwa ga masu sari akan 835 kan kowace Lita maimakon 865 kan kowace Lita da ake sayarwa a baya. A ranar Laraba ne dai matatar man ta sanar da abokan huldarta da rage wannan sabon farashin. Wannan ne karo na 3 da matatar man ta Dangote ke rage farashin man ta a cikin makonni 6 da suka gabata.
Mu ne ke kulla rikicin dake faruwa a jam’iyyun Adawa>>Jam’iyyar APC

Mu ne ke kulla rikicin dake faruwa a jam’iyyun Adawa>>Jam’iyyar APC

Duk Labarai
Wani Jigo a jam'iyyar APC ya bayyana cewa, jam'iyyarsu ce ke da alhakin rikicin dake faruwa a jam'iyyun Adawa. Hon. Farouk Adamu Aliyu ne yayi wannan magana inda yace sun yi hakanne kamin zuwa zaben shekarar 2027. Wannan magana tasa dai ta zo daidai da Hasashen da mutane ke yi na cewa dama APC ce ke hana jam'iyyun Adawar zaman lafiya dan kada su bata kalubale. Ya bayyana hakanne hirar da aka yi dashi a gidan Talabijin na AIT. Yace tabbas sune ke hana jam'iyyun na adawa zaman lafiya dan ba zasu bari su kwace mulki a hannunsu ba, yace a yanzu ma babu wata jam'iyyar Adawa ta gaskiya duk suna hauragiya ne amma babu wata jam'iyyar adawa da zata iya kwace mulki a hannun APC, saidai watakila nan gaba.
Karanta Jadawalin Shuwagabannin sojojin da aka Taba yi a Najeriya

Karanta Jadawalin Shuwagabannin sojojin da aka Taba yi a Najeriya

Duk Labarai
-1). Lt. Col. Yakubu Gowon( January 1966 – July 1966-Corps: Infantry.-State of Origin: Plateau State -2). Lt. Col. Joseph Akahan( August 1966 – May 1967).-Corps: Infantry-State of Origin: Benue State -3). Maj. Gen. Hassan Katsina( May 1968 – January 1971).-Corps: Armoured-State of Origin: Katsina State -4). Maj. Gen. David Ejoor( January 1971 – July 1975).-Corps: Infantry-State of Origin: Delta State -5). Lt. Gen. Theophilus Danjuma( July 1975 – October 1979).-Corps: Infantry-State of Origin: Taraba State -6. Lt. Gen. Ipoola Alani Akinrinade( October 1979 – April 1980).-Corps: Infantry-State of Origin: Osun State -7. Lt. Gen. Gibson Jalo( April 1980 – October 1981 ).-Corps: Infantry-State of Origin: Adamawa State -8 ). Lt. Gen. Mohammed Inuwa Wushishi( October 1981 – O...
Hotuna: Kalli Yanda aka hadawa Dangote Kek din murnar ranar Haihuwarsa na manyan motoci da ya kayatar

Hotuna: Kalli Yanda aka hadawa Dangote Kek din murnar ranar Haihuwarsa na manyan motoci da ya kayatar

Duk Labarai
Wata mata me dafa Kek, ta hadawa Aliko Dangote kek dan murnar zagayowar ranar Haihuwarsa. Dangote dai ya cika shekaru 68 inda mutane ciki hadda Shugaban kasar Najeriya suka tayashi murna. Matar ta nuna irin Kek din da ta shiryawa Aliko Dangote wanda ya hada dana motoci dana matatar mansa da sauransu. Mutane da yawa sun yi mamakin ganin Kek din. https://www.youtube.com/watch?v=bPjOjEu2d0o Aliko Dangote dai shine na farko da yafi kowa Kudi a Afrika.
An min Wahayi, Allah ya gayamin kada in sake in aske gashin kaina>>Inji Fasto Jimmy Odukoya bayan da ake ta kiraye-kirayen ya aske kitson da yayi a kansa

An min Wahayi, Allah ya gayamin kada in sake in aske gashin kaina>>Inji Fasto Jimmy Odukoya bayan da ake ta kiraye-kirayen ya aske kitson da yayi a kansa

Duk Labarai
Fasto Jimmy Odukoya na cocin Fountain of Life church ya bayyana cewa, An masa wahayi inda Allah ya gaya masa kada ya sake ya aske gashin kansa. Faston ya bayyana wa mabiyansa hakane a gaban mabiyansa yayin da yake musu wa'azu. Yace kanwarsa ta bashi shawarar aske gashin kansa musamman saboda kada mutane su rika masa wani irin kallo. Saidai yace bai yanke shawara ba sai da ya nemi taimakon Allah kuma an masa wahayi inda aka ce kada ya aske gashin kan. Yace ya tura kanwar tasa ma yace ta je ta yi addu'a akai inda ta dawo tace itama an mata wahayi cewa kada ya aske gashin kan nasa. Inda ya bata amsar cewa shima dama an gaya masa.
Kalli Bidiyo: A karshe dai Shaikh Adam Muhammad Albany Gombe yawa Dan Bello Tonon sililin da yace zai masa

Kalli Bidiyo: A karshe dai Shaikh Adam Muhammad Albany Gombe yawa Dan Bello Tonon sililin da yace zai masa

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Sheikh Adam Muhammad Albany Gombe ya yiwa shahararren dan soshiyal Midiya, Dan Bello Tonon Sililin da ya yi Alkawarin yi masa. Hakan ya biyo bayan labarin da Dan Bello ya wallafa ne na zargin shugaban Izala, Sheikh Bala Lau da aikata ba daidai ba da dukiyar gina ajujuwan karatu. A martanin Sheikh Adam yace Dan Bello bashi da alaka da wani babban malami ko makaranta dan haka bai ga dalilin da zai sa wanda bashi da ilimin addini mutane su rika daukar labari daga wajansa ba. htt...