Monday, February 23
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Shahararriyar ‘yar fim din kudu, Destiny Etiko da aka saba gani sanye da kaya tsirara-tsirara ta yi bayanin dalilin da ya sa ta sanya Hijabi a cikin watan Azumi

Shahararriyar ‘yar fim din kudu, Destiny Etiko da aka saba gani sanye da kaya tsirara-tsirara ta yi bayanin dalilin da ya sa ta sanya Hijabi a cikin watan Azumi

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Turaruwar fina-finan Kudu, Destiny Etiko da aka saba gani sanye da kaya tsirara-tsirara a cikin watan Azumi sai gata sanye da Hijabi. Abin ya baiwa masoyanta mamaki inda akai ta tambayarta menene dalili. A cikin wani bidiyo data wallafa a shafinta na sada zumunta, ta fadi daliinta na yin hakan. Tace wani fim ne ta fito a ciki a matsayin bahaushiya, shiyasa ake ta ganinta sanye da Hijabi kwana biyu.
Allah ko a Lahira karkaba mijina matan Hurul ayn kodaya sabida za’a iya samun matsala, wlh na tsani kishiya>>Inji Fatima

Allah ko a Lahira karkaba mijina matan Hurul ayn kodaya sabida za’a iya samun matsala, wlh na tsani kishiya>>Inji Fatima

Duk Labarai
Wata Matashiya me suna Fatima ta jawo cece-kuce sosai a kafafen sada zumunta inda take wa mijinta fatan ko a Lahira kada Allah ya baiwa mijinta Hurul ayn. Ga abinda ta rubuta kamar haka: "Allah ko a Lahira karkaba mijina matan Hurul ayn kodaya sabida za'a iya samun matsala, wlh na tsani kishiya" Da yawa dai sun mayar mata da martanin wannan addu'a bata dace ba.
Kaso 90 cikin 100 na Kiristocin da ake ķķàshèwà a Duniya a Najeriya ake ķķàshèsu, Najeriya ta kasa baiwa Kiristoci kariya dan haka zamu Kakaba mata Takunkumi>>Inji Kasar Amurka

Kaso 90 cikin 100 na Kiristocin da ake ķķàshèwà a Duniya a Najeriya ake ķķàshèsu, Najeriya ta kasa baiwa Kiristoci kariya dan haka zamu Kakaba mata Takunkumi>>Inji Kasar Amurka

Duk Labarai
Majalisar kasar Amurka ta baiwa shugaban kasar, Donald Trump shawarar ya kakabawa Najeriya takunkumi saboda yawan kashe kiristoci da ake yi a kasar. Majalisar ta cimma wannan matsayane bayan samun bayanai daga wani bincike da aka gudanar da yake nuna cewa kaso 90 na kiristocin da ake kashewa a Duniya a Najeriya ne hakan ke faruwa. Majalisar ta kasar Amurka ta zargi Najeriya da kasa daukar matakan da suka kamata dan baiwa Kiristocin kariya daga hare-haren ta'addanci dake yin sanadiyyar mutuwarsu. Saidai a martanin Gwamnatin Najeriya tace wannan magana ba gaskiya bace. Sanarwar da ma'aikatar harkokin kasashen waje ta Najeriya ta fitar ta hannun kakakinta, Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya bayyana cewa, tabbas akwai matsalar tsaro a Najeriya. Amma ba wani addini daya aka ware shi k...
Hukumar babban birnin tarayya, Abuja ta kwacewa PDP filinta da babban Ofishinta na kasa dake Abuje ke gine

Hukumar babban birnin tarayya, Abuja ta kwacewa PDP filinta da babban Ofishinta na kasa dake Abuje ke gine

Duk Labarai
Hukumar kula da babban birnin Tarayya, Abuja, FCTA ta kwace filin hedikwatar jam'iyyar PDP dake Abuja. A takardar kwace filin da hutudole ya karanta, hukumar FCTA tace PDP taki biyan harajin da ya kamata ta biya na kan filin kusan tsawon shekaru 20 da suka gabata kenan. Kuma tun shekarar 2023 ake ta tunatar da PDP game da biyan harajin amma ta yi kunnen uwar shegu. Dan hakane yanzu an kwace filin ya zama mallakin hukumar FCTA din dake Abuja.
Banda mu a cikin wadanda suka saci man fetur daga tankar mai data fadi, Bidiyon karyane ake yadawa>>Inji Hukumar ‘yansandan Najeriya

Banda mu a cikin wadanda suka saci man fetur daga tankar mai data fadi, Bidiyon karyane ake yadawa>>Inji Hukumar ‘yansandan Najeriya

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan Najeriya ta musanta cewa an ga jami'anta suna kwasar man fetur bayan da wata tankar mai ta fadi. Bidiyo ya watsu sosai inda aka ga wasu da kayan 'yansandan suma sun shiga sahu masu satarman daga tankar. Saidai a sanarwar da kakakin hukumar 'yansandan ta kasa, Olumuyiwa Adejobi ya fitar, yace ba 'yansandan Najeriya ne ba a bidiyon, 'yansandan makwabtan Najeriya ne. Ya kara da cewa, an saki Bidiyonne kawai dan a batawa hukumar 'yansandan Najeriya suna. Yace jami'an tsaron dake bidiyon, faransanci suke ba Turanci ba yace dan haka ba 'yansandan Najeriya bane. Yace hukumar 'yansanda tana nan kan gudanar da aikinta bisa doka da kwarewa. Ya gargadi mutane su daina yada labarin da bai inganta ba.
Girman kai da haushine cike da zuciyar El-Rufai saboda bai samu Minista ba shiyasa ya koma SDP>>Inji APC

Girman kai da haushine cike da zuciyar El-Rufai saboda bai samu Minista ba shiyasa ya koma SDP>>Inji APC

Duk Labarai
jam'iyyar APC ta caccaki tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai inda ta bayyanashi a matsayin wanda ke ci ke da girman kai da haushi saboda bai samu mukamin minista ba. Sakataren jam'iyyar, Felix Morka ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar. Yace El-Rufai ya kamata idan zai soki gwamnatin Tinubu yayi suka ta adalci. Felix yayi watsi da ikirarin El-Rufai na cewa jam'iyyar APC ta kauce daga kan turbar da aka kafata inda yace gwamnatin Tinubu ta samu ci gaba sosai da suka hada da cire tallafin man fetur da daidaita canjin kudi da sauransu.
Majalisar mu ta dattijai kamar kungiyar tsafi take, kowane Sanata na tsoron ya soki kakakin majalisa, Akpabio ya taba rike min hannu ya rika murzawa, kowace mace akawa haka tasan abinda ake nufi>>Sanata Natasha Akpoti ta sake yiwa Akpabio tonon silili

Majalisar mu ta dattijai kamar kungiyar tsafi take, kowane Sanata na tsoron ya soki kakakin majalisa, Akpabio ya taba rike min hannu ya rika murzawa, kowace mace akawa haka tasan abinda ake nufi>>Sanata Natasha Akpoti ta sake yiwa Akpabio tonon silili

Duk Labarai
Har yanzu dai Sanata Natasha Akpoti bata saurara ba da yiwa kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio tonon silili. A sabuwar hirar da ta yi da BBC Pidgin, Natasha tace majalisarsu kamar kungiyar tsafi take. Tace kowane sanata na tsoron ya bayyana ra'ayin da ya sha banban da na kakakin majalisar saboda tsoron kada a saka masa ido. Tace amma zargin da takewa Sanata Godswill Akpabio da gaskene, ta sake maimaita cewa akwai sanda suka je gidansa ya kama hannunta a gaban mijinta ya ja ya suna tafiya, tace ya rika murza mata hannu, tace kowace mace akawa haka tasan abinda ake nufi. Tace hakanan akwai sanda ta manta ta tafi aiki da sauri bata dauki zoben alkawarinta na aure ba, tace Sanata Godswill Akpabio na ganinta sai yake ce mata yaya Natasha, naga baki saka zoben aurenk...
Dan Fim Din Kudu ya bayar da labarin yanda abokan aikinsa mata 3 suka masa fyàdè a yayin da suke wani otal daukar fim

Dan Fim Din Kudu ya bayar da labarin yanda abokan aikinsa mata 3 suka masa fyàdè a yayin da suke wani otal daukar fim

Duk Labarai
Dan fim din kudu, Lanre Adediwura ya bayyana yanda wasu mata 3 abokan aikinsa suka masa fyade a yayin da yaje aikin daukar wani fim. Yace da farko dai ya je wajan daukar fim dinne inda daga baya wata abokiyar aikinshi ta sameshi ta bayyana masa cewa, tana sonsa. Yace a nan ya sanar da ita yana da aure amma tace ta ji ta gani. Ya kara da cewa anan suka zauna suna buga karta ko wasan kati, da suka gama dare yayi, ya manta katin a hannunta. Yace ta je dakin otal dinsa dan ta kai masa katin, inda anan ne ya ganta da abokanta biyu sun je su masa fyade. Ya bayyana hakane a shafinsa na sada zumunta inda lamarin ya jawo cece-kuce.
A kudancin Kaduna, Gwamnatin mu ta APC bata tabuka abin Arziki ba>>Inji Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima

A kudancin Kaduna, Gwamnatin mu ta APC bata tabuka abin Arziki ba>>Inji Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima

Duk Labarai
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayyana cewa, Gwamnatinsu ta APC bata tabuka abin a zo a gani ba a kudancin jihar kaduna. Ya bayyana hakane a matsayin suka ga gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. El-Rufai ya shafe shekaru 8 yana a matsayin gwamnan Kaduna saidai a kwanannan ya bar jam'iyyar APC zuwa PDP. A ci gaba da bayaninsa, Kashim Shettima ya bayyana cewa, Amma gwamnatin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta canja akalar yankin inda ta kawo mai ci gaba. Ya bayar da misali na ci gaban da gwamnatin Tinubu ta kai yankin kudancin jihar Kaduna inda yace kwanannan Shugaba Tinubun ya sakawa kudirin dokar samar da jami'ar kimiyya da fasaha ta Federal University of Applied Sciences hannu wadda za'a bude a karamar hukumar Kachia.
El-Rufai ya zargi Gwamna Uba Sani na Kaduna da sace kudaden kananan hukumomi ya je kasashen Ingila da Afrika ta kudu ya sayi gidaje

El-Rufai ya zargi Gwamna Uba Sani na Kaduna da sace kudaden kananan hukumomi ya je kasashen Ingila da Afrika ta kudu ya sayi gidaje

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya zargi Gwamnan jihar me ci, Malam Uba Sani da yin amfani da kudaden kananan hukumomi ya sayi gidaje a kasashen Seychelles, South Africa, da the United Kingdom.  EL-RUFAI wanda bai dade da barin jam'iyyar APC zuwa SDP ba ya bayyana hakane a yayin hirar da aka yi dashi a gidan rediyon Najeriya dake Kaduna ranar Talata. Yace gwamna Uba Sani na karkatar da kudaden kananan hukumomi inda yake canjasu zuwa dala bisa shirin sayen gidaje. Yace amma shi a zamanin mulkinsa ba abinda yayi kenan ba. Yace a zamaninsa suna baiwa kananan hukumomi kudadensu, yace shuwagabannin kananan hukumomi na APC da PDP duk suna nan da rai kuma zasu iya bayar da shaida akan hakan. Yace amma hukumomin gwamnatin tarayya sun ki cewa uffan kan abinda...