Mun kusa ƙaddamar da haɗakar kawar da APC – Ƴan adawa
Manyan ƴan siyasar Najeriya da ke jagorantar shirin yin haɗaka tsakanin jam'iyyun hamayya domin tunkarar APC a zaɓen 2027, sun mayarwa ƙungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP martani, a kan matsayar da gwamnonin suka ɗauka cewa ba su goyon bayan ƙulla duk wata haɗaka da za ta fitar da su daga PDP.
Gamayyar ƴan adawar da ta haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar Labour a zaɓen 2023 da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai da dai sauran ƴan siyasa, ta ce nan ba da jimawa ba za a sanar da ƙulla sabuwar haɗakar siyasa da za ta ceto Najeriya daga mulkin APC.
Ɗaya daga cikin jagororin tafiyar ƙulla sabuwar haɗakar siyasar ta Najeriya kuma tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar APC na ƙasa mai kula da shiyyar Arewa Maso Yamma, Sali...








