Sunday, February 22
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Addinin mu na kirista yafi samun hutu da yawa a tsarin Ilimin Najeriya fiye da Musulunci, dan haka ku janye maganar zuwa kotu akan bayar da hutun Azumin watan Ramadana>>Reno Omokri ga kungiyar Kiristoci ta CAN

Addinin mu na kirista yafi samun hutu da yawa a tsarin Ilimin Najeriya fiye da Musulunci, dan haka ku janye maganar zuwa kotu akan bayar da hutun Azumin watan Ramadana>>Reno Omokri ga kungiyar Kiristoci ta CAN

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohon hadimin shugaban kasa, Reno Omokri ya bayyana cewa, Kiristoci yafi addinin Musulunci amfana da hutu da ake a tsarin ilimi na Najeriya. Ya kara da cewa, Ana hutun sabuwar shekara, ana hutun Easter, hakanan ana hutun Kirsimeti sannan kuma tsarin ilimin gaba daya kusan akan tsarin Kiristanci yake amma Musulmai sun hakura suna aiki dashi. Yace idan kungiyar CAN ta ce zata kai kara, to hakan zai sa suma musulmai su dauki matakin ramuwa, yace idan har CAN tana son ta yi magana ...
Manyan ‘yansanda 2 sun ki ajiye aiki duk da basu umarnin hakan bayan gani cewa sun yi karyar shekaru

Manyan ‘yansanda 2 sun ki ajiye aiki duk da basu umarnin hakan bayan gani cewa sun yi karyar shekaru

Duk Labarai
' Manyan 'yansandan Najeriya 2 da aka gano sun yi karyar shekaru kuma aka basu umarnin ajiye aiki, suki ajiye aikin. 'Yansandan sune, Idowu Owohunwa, dake Zone 12 a jihar Bauchi sai kuma DCP Simon Lough. An gano 'yansanda da yawa da ko dai sun yi karyar shekaru ko kuma sun canja shekarun barin aikinsu a takardunsu na gidan aikin dansandan. Kuma su wadannan 'yansanda biyu da suka ki ajiye aiki suna ciki. 'Yansanda 7 masu mukamin DIG ne suka ajiye mukamansu bayan da kokarinsu na kara shekarun aiki yaci tura.
Dukkan alamu sun nuna Jam’iyyar mu ta kama hanyar rugujewa>>PDP

Dukkan alamu sun nuna Jam’iyyar mu ta kama hanyar rugujewa>>PDP

Duk Labarai
Wasu masu ruwa da tsaki a jami'iyyar PDP sun koka da cewa Jam'iyyar ta kama hanyar rugujewa inda suka yi kira ga 'yan Jam'iyyar a dukkan fadin Najeriya da su tashi tsaye dan cetota. Sun bayyana hakane a wajan wani taro da ya gudana a Abuja ta bakin wakilinsu, Obinna Nwachukwu. Ya bayyana cewa, akwai bukatar 'yan Jam'iyyar daga kowane sashe na kasarnan su fito dan yunkurin hanata durkushewa. Yace lokaci yayi da zasu daina rungume hannu suna ganin yanda wasu 'yan Jam'iyyar suke mata zagon kasa, wasu ma daga ciki har mukami aka basu a Jam'iyya me mulki ta APC suna ayyuka da kalamai na kokarin ruguza PDP. Yace Jam'iyyar PDP itace wadda talaka ya dogara da ita a matsayin Jam'iyyar adawa wadda zata kalubalanci Jam'iyyar APC me mulki da kwatowa talaka 'yancinsa.
Darajar Naira ta fadi a kasuwar Chanji

Darajar Naira ta fadi a kasuwar Chanji

Duk Labarai
Naira ta samu tasgaro a kasuwar Chanji inda ta fadi zuwa N1,510 akan kowace dala a jiya. Wanan farashi yayi sama idan aka kwatanta da yanda aka kulle kasuwar a makon da ya gabata inda Nairar ke akan farashin N1,505. Saidai a kasuwar Gwamnati Nairar tashi ta yi inda aka sayi dala akan N1,499. Za'a iya fahimtar hakan idan aka yi la'akari da farashin da aka kulle kasuwar a makon da ya gabata na N1,500 akan kowace dala.
Hotuna: Ɗan gidan shugaban shugaban kasa, Seyi Tinubu, ya gudanar da shan ruwa tare da yan siyasa da sauran al’umma a jihar Kano

Hotuna: Ɗan gidan shugaban shugaban kasa, Seyi Tinubu, ya gudanar da shan ruwa tare da yan siyasa da sauran al’umma a jihar Kano

Duk Labarai
Ɗan gidan shugaban shugaban kasar Najeriya Seyi Tinubu, ya gabatar da shan ruwa tare da yan siyasa da sauran al'umma a jihar Kano. Cikin wadanda suka halarci taron shan ruwan da Seyi Tinubu, ya shirya akwai yan jam'iyyar NNPP mai adawa da APC. Shima shugaban jam'iyyar NNPP na jihar Kano Hashimu Dungurawa, ya halarci wajen shan ruwan.
Mata a jihar Bayelsa sun fito zanga-zanga inda suka ce Sanata Natasha Akpoti ta janye ‘sharrin’ da tawa Sanata Godswill Akpabio

Mata a jihar Bayelsa sun fito zanga-zanga inda suka ce Sanata Natasha Akpoti ta janye ‘sharrin’ da tawa Sanata Godswill Akpabio

Duk Labarai
Wata kungiyar mata daga yankin Kudu maso kudu a jihar Bayelsa ta fito zanga-zanga akan rikicin sanata Natasha Akpoti da Godswill Akpabio. Kungiyar matan tace kada Sanata Natasha Akpoti ta zubarwa da Sanata Godswill Akpabio mutuncinsa da ya dade yana karewa. Sun yi Allah wadai da halinta inda suka ce ba irin halin matan Najeriya bane, kamar yanda daya daga cikin matan me suna Hon. Ebiere Akpobasa ta bayyana.
Babban Dansandan Najeriya da aka yi Gàrkùwà dashi a Abuja ya kubuta

Babban Dansandan Najeriya da aka yi Gàrkùwà dashi a Abuja ya kubuta

Duk Labarai
Rundunar 'yansandan Najeriya a Abuja babban birnin Najeriya ta ce jami'inta da aka bayar da rahotonnin cewa an sace ya koma gida tuni. Da take tabbatar wa da BBC ta wayar tarho, kakakin rundunar Josephine Addeh ta ce da ma ba wani mummunan abu ne ya faru da Sufuritanda Modestus Ojiebe ba. "Motarsa ce ta samu matsala kawai a kan hanya, kuma gaba ɗaya abin da ya faru bai fi 'yan awanni ba ya kuɓuta kuma ya koma gida," in ji ta. Tun da farko was kafofin yaɗa labarai sun ruwaito cewa motar ɗansandan ce ta samu matsala a kan babban titin Abuja zuwa Kaduna, inda wasu da ake zargin masu garkuwa ne suka yi awon gaba da shi.
Tinubu ya amince da kasafin kammala titin Abuja-Kano cikin wata 12

Tinubu ya amince da kasafin kammala titin Abuja-Kano cikin wata 12

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ba da umarnin kammala aikin babbar hanyar Abuja zuwa Kano cikin wata 12. Mai magana da yawun fadar shugaban Najeriya, Sunday Dare, ya ce a yau Litinin shugaban ya amince bayar da umarnin. "Shugaba Tinubu ya amince da kasafin kammala wuraren da ba a gama ba a kan titin Abuja-Kaduna, da na Kaduna-Zaria cikin wata 12," kamar yadda ya wallafa a shafinsa na dandalin X. Ya ƙara da cewa "wannan titi ne mai muhimmanci ne a kodayaushe". A watan Janairu gwamnatin Bola Tinubu ta sanar da bai wa wani sabon kamfani ƙarashen aikin titin bayan ta ƙwace kwangilarsa daga hannun Julius Berger.
An mai daurin shekaru 14 saboda ya cire kwandam ba tare da budurwarsa ta sani ba yayin da suke jima’i

An mai daurin shekaru 14 saboda ya cire kwandam ba tare da budurwarsa ta sani ba yayin da suke jima’i

Duk Labarai
An daure wani direban babbar mota tsawon shekaru 14 saboda ya cire kwandam yayin da yake jima'i da budurwarsa ba tare da ta sani ba. Wannan mutumi me suna Laurence Rafter, dan kimanin ahekaru 43, ya hadu da wadda yawa wannan laifi me shekaru 32 a wata kafar sadarwa ta yanar gizo ne. Saidai ya bata sunan karya da Address din karya sannan yace mata yana da katon gidan Alfarma. Hakanan sun hadu inda suka yi jima'i amma kamin su fara ta gaya masa cewa yasa kwandam, kuma ya yadda ashe suna cikin yi ya cire bata sani ba. Bayan sun rabu ya ce mata yana dauke da cutar kan jamau amma daga baya aka gane karya yake kawai dan ya bata tsorone, mutumin dake zaune a north London an daureshi shawon shekaru 14 bayan samunsa da laifi.