Karyace:Fubara ya mayarwa da shugaba Tinubu martani bayan da yace bai tabuka komai ba yayin da aka kaiwa Bututun man fetur din Najeriya hari
Gwamnan jihar Rivers da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dakatar, Simi Fubara ya bayyana cewa ba gaskiya bane ikirarin da shugaban kasa yayi na cewa bai tabuka komai ba kan matsalar tsaron da ta kunno kai a jihar.
Ya kuma karyata ikirarin shugaban kasar na cewa ya rushe majalisar jihar Rivers ba tare da gina wata ba.
A martanin da ya mayar ta hannun me magana da yawunsa,Nelson Chukwudi Gwamna Fubara ya bayyana cewa, abin mamakine fadar shugaban kasar na magana akan abinda basu da masaniya akansa.
Yace ko da yake ya dora Alhakin hakan akan masu baiwa shugaban kasar bayanai wanda sune suka kasa bashi bayana da ya kamata yayi amfani dasu wajan yin shawara.
Fubara yace maganar da tsohon gwamnan jihar, kuma ministan Abuja a yanzu, Nyesome Wike yayine tasa aka kai harin.
Yace ...








