Rayuwar Sayyadina Umar Da Ayyukansa Na Yada Addinin Musulunci
Cikakken Sunansa da Asalinsa
Sunansa Umar Dan Khaddabi Dan Nufail Dan Abdul Uzza Dan Rayahi Dan Abdullahi Dan Kurdi Dan Razahi Dan Adiyyu Dan Ka’abu Dan Lu’ayyu Dan Galibu al Adawi al Kurashi. Ya hadu da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama a zumunci ta wajen kakansa na Takwas, wato Ka’abu Dan Lu’ayyu, wanda shi ne kakan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama na bakwai.
Mahaifiyarsa ita ce Kanwar Abu Jahli, Hantamah diyar Hisham Dan Mughirah daga kabilar Makhzum.
Haifuwarsa:
An haifi Sayyidina Umar Radiyallahu Anhu bayan yakin nan da aka fi sani da Harbul Fijar, a shekara ta Arba’in da uku kafin hijira. Don haka Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya girme shi da shekaru goma cif.
Siffarsa da Dabi’unsa:
An siffanta Sayyidina Umar Radiyallahu Anhu da cewa, mutum...






