Saturday, March 15
Shadow

Ban san an kama kananan yara ba>>Gwamna Abba Kabir Yusuf

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayyana farin cikinsa da sakin kananan yara da aka kama bisa zargin cin amanar kasa.

Gwamnan yace bai san an kama yaran ba sai bayan da aka kaisu gaban kotu a Abuja.

Ya bayyana hakane a Asibitin Muhammadu Buhari Special Hospital inda aka kai yaran dan a dubasu a tabbatar suna cikin koshin lafiya.

Gwamnan ya kuma godewa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kan yafewa yaran inda yace zai tabbatar an sada su da iyalansu sannan a tabbatar sun koma makaranta dan Inganta rayuwarsu.

Karanta Wannan  Man Fetur din matatar man Dangote ba zai ishi Najeriya ba dan haka zamu ci gaba da Shigo da man fetur daga kasar waje>>inji NNPCL da 'yan kasuwar Man Fetur

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *