Tuesday, February 24
Shadow

Ban san an kama kananan yara ba>>Gwamna Abba Kabir Yusuf

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayyana farin cikinsa da sakin kananan yara da aka kama bisa zargin cin amanar kasa.

Gwamnan yace bai san an kama yaran ba sai bayan da aka kaisu gaban kotu a Abuja.

Ya bayyana hakane a Asibitin Muhammadu Buhari Special Hospital inda aka kai yaran dan a dubasu a tabbatar suna cikin koshin lafiya.

Gwamnan ya kuma godewa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kan yafewa yaran inda yace zai tabbatar an sada su da iyalansu sannan a tabbatar sun koma makaranta dan Inganta rayuwarsu.

Karanta Wannan  Akwai Wanda Ya Yi Minista Mai Lasisi Amma Ba Za Ka Nuna Masallaci Guda Daya Da Ya Gina A Jihar Gombe Ba, Ko Yake Daukar Nauyin Wasu Limamai Ko Ladanai Ba, Cewar Sheik Albanin Gombe, ko kun san da wa yake?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *