Saturday, December 13
Shadow

Ban san ta yaya suke iya bacci ba yayin da ‘yan tà’àddà ke kàshè mutane>>Atiku ya koka kan matsalar tsaro, yace shuwagabannin da suka zo bayan mulkinsu shi da Obasanjo ne suka kawo matsalar tsaro

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bayyana cewa, shuwagabannin Najeriya da suka zo bayan Obasanjo ne ke da Alhakin dawowar Kungiyar Bòkò Hàràm.

Ya bayyana hakane a Abuja a yayin ziyarar da wasu ‘yan siyasa daga jihar Kogi suka kai masa.

Yace kungiyar ta fara bayyanane a shekarar 2002 a jihar Yobe

Yace suna sumun labari, Obasanjo ya aika aka kirashi yace mai ya yake ganin za’a bullowa wannan lamari? Sai yace masa a kira shuwagabannin tsaro a basu lokaci su gama da kungiyar, idan suka kasa sai a sauke su a nada wasu.

Yace haka kuwa aka yi kuma aka murkushe kungiyar.

Yace bayan sun sauka Mulki ne wanda suka hau suka yi sakaci kungiyar ta dawo.

Karanta Wannan  Bayan watanni 3 Dangote ya koma siyo man fetur daga kasar Amurka

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *