Saturday, December 13
Shadow

Bidiyo: Kalli Yanda Yahudawan Israela suka yiwa Hezubollahh kutse a wayoyinsu suka tayar musu da bamabamai a cikin wayar kowanne

Yahudawan Israela sun yi wani abin ban mamaki da ya dauki hankulan Duniya.

A ci gaba da yakin da suke da Falasdinawa, sanannen abune cewa, Hezbollah sun shigarwa Falasdinawan fadan inda suka ce idan ba’a daina kashe Falasdinawan ba suma ba zasu daina fada da Israela ba.

https://twitter.com/sentdefender/status/1836069676373196808?t=hnPtRc7J8rXUtQFIeDudfA&s=19

A hakanne kasar Israela ta tayarwa da mayakan Hezbollah da bamabamai a cikin wayoyinsu.

Akalla mutane Dubu 2 ne suka jikkata sadaniyyar tashin wadannan bamabamai a fadin kasar ta Lebanon ciki hadda wakilin kasar Iran a Lebanon din kamar yamda wasu rahotanni suka bayyanar.

Karanta Wannan  An kaddamar da shafin Yanar gizo na masoya Shugaba Tinubu, da ke da ra'ayin sake zabensa a 2027 duk wanda ke da ra'ayi yana iya zuwa yayi rijista

Saidai duk da lamarin tayar da bamabamai din ya dauki hankula, abu daya da aka rika tambaya shine,wai me yasa kasar Israela ta rikawa falasdinawa kisan kiyashi idan dai zata iya amfani da irin wannan hanyar dan kashe wadanda take so?

Watakila amsar wannan tambayar itace Hezbollah tafi Hamas karfi wadda idan Israela tace zata yi fada da ita na kai tsaye, itama zata ji a jikinta.

Karanta Wannan  Za'a biya matasa da suka kammala Bautar Kasa karin kudin Naira 77,000>>Inji Hukumar NYSC

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *