Tuesday, August 18
Shadow

Bidiyo: Kalli Yanda Yahudawan Israela suka yiwa Hezubollahh kutse a wayoyinsu suka tayar musu da bamabamai a cikin wayar kowanne

Yahudawan Israela sun yi wani abin ban mamaki da ya dauki hankulan Duniya.

A ci gaba da yakin da suke da Falasdinawa, sanannen abune cewa, Hezbollah sun shigarwa Falasdinawan fadan inda suka ce idan ba’a daina kashe Falasdinawan ba suma ba zasu daina fada da Israela ba.

https://twitter.com/sentdefender/status/1836069676373196808?t=hnPtRc7J8rXUtQFIeDudfA&s=19

A hakanne kasar Israela ta tayarwa da mayakan Hezbollah da bamabamai a cikin wayoyinsu.

Akalla mutane Dubu 2 ne suka jikkata sadaniyyar tashin wadannan bamabamai a fadin kasar ta Lebanon ciki hadda wakilin kasar Iran a Lebanon din kamar yamda wasu rahotanni suka bayyanar.

Karanta Wannan  An kama tsaffin shuwagabannin kamfanin man Fetur na kasa da aka sauke satin da ya gabata bisa zargin sun sace kudaden da aka ware dan gyaran matatun man Najeriya, An gano Naira Biliyan 80 a Asusun daya daga cikinsu

Saidai duk da lamarin tayar da bamabamai din ya dauki hankula, abu daya da aka rika tambaya shine,wai me yasa kasar Israela ta rikawa falasdinawa kisan kiyashi idan dai zata iya amfani da irin wannan hanyar dan kashe wadanda take so?

Watakila amsar wannan tambayar itace Hezbollah tafi Hamas karfi wadda idan Israela tace zata yi fada da ita na kai tsaye, itama zata ji a jikinta.

Karanta Wannan  'Yan Najeriya da yawa na zuwa banki dan dakatar da aika musu sakon hadadar kasuwanci watau Alert saboda kudin da bankin ke cire musu yayi yawa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *