Wednesday, February 25
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyo: A karshe dai Tauraruwar fina-finan Hausa, Khadija MaiNumfashi ta fito daga hannun ‘yansanda inda tace fhadanta da Marwat ya kare

Kalli Bidiyo: A karshe dai Tauraruwar fina-finan Hausa, Khadija MaiNumfashi ta fito daga hannun ‘yansanda inda tace fhadanta da Marwat ya kare

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Khadija MaiNumfashi ta sanar da fitowarta daga hannun 'yansanda bayan da aka kamata. Tace Kabiru Legas ne ya je wajan 'yansanda yace an yiwa rayuwarsa barazana inda aka tambayeshi wa yake zargi yace ita yake zargi. Tace dan haka dole ne yasa aka kirata amma Allah ya wanke ta. A karshe ta yi godiya ga masoyanta da abokan sana'arta da 'yan uwa bisa irin soyayyar da aka nuna mata.
Da Duminsa: An kama karin sojoji 26 bisa zarginsu da hannu a yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki

Da Duminsa: An kama karin sojoji 26 bisa zarginsu da hannu a yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa yawan sojojin da ake tsare dasu ana bincikensu kan zargin hannu a yunkurin yiwa shugaba Tinubu juyin mulki sun kai 42. A baya dai rahotanni sun ce sojoji 16 ne aka kama ake bincike. Saidai a yanzu yawan sojojin sun kai 42 wanda ake bincike kamar yanda jaridar Daily Trust ta ruwaito. Jaridar tace wasu majiyoyi a gidan sojin sun sanar da ita cewa, ana gayyatar manyan sojoji inda ake musu tambayoyi game da zargin hannu a yunkirin juyin mulkin.
Sabbin Bayanai sun sake fitowa game da sojojin da ake zargin sun yi yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki

Sabbin Bayanai sun sake fitowa game da sojojin da ake zargin sun yi yunkurin yiwa shugaba Tinubu Jhuyin mulki

Duk Labarai
Sabbin Bayanai sun sake fitowa game da sojojin da ake zargin sun yi yunkurin yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu Juyin mulki. Kafar Premium times ta bayyana cewa, a cikin sojojin guda 16 da ake tsare dasu akwai Brigadier General daya da Conel daya da Lieutenant Colonel guda 4, sai masu mukamin Major 5 sai masu mukamin Captain 2, sai mai mukamin Lieutenant daya. Guda 14 daga cikinsu sojojin kasa ne sai sauran akwai sojan ruwa dana sama. Saidai har yanzu jaridar bata bayyana sunayensu ba. Wata majiya dai tace an kama karin sojoji da ake zargi da hannu a lamarin bayan su.
Da Duminsa:Duka ‘yan majalisar wakilai daga jihar Enugu sun koma jam’iyyar APC daga PDP

Da Duminsa:Duka ‘yan majalisar wakilai daga jihar Enugu sun koma jam’iyyar APC daga PDP

Duk Labarai
Duka 'yan majalisar wakilai da suka fito daga jihar Enugu sun bar jam'iyyar PDP zuwa APC. Kakakin Majalisar, Tajudeen Abbas ne ya sanar da haka a zaman majalisar na ranar Alhamis. Gwamnan jihar Enugu, Peter Mba ya shaida wannan lamari a majalisar. 'Yan majalisar sun ce sun koma APC ne saboda jam'iyyar su ta PDP rikicin cikin gida na neman gamawa da jam'iyyar.
Dan Majalisa, Honarabul Musa Lawal Maja Kura daga jihar Yobe na daukar Hankula bayan ganin tsaffon hotunansa shekaru 2 da suka gabata

Dan Majalisa, Honarabul Musa Lawal Maja Kura daga jihar Yobe na daukar Hankula bayan ganin tsaffon hotunansa shekaru 2 da suka gabata

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} IKON ALLAH: Cikin Shekara Biyu Wannan Dan Majalisar Ya Murmure Ya Koma Haka Dan majalisar jiha ne da yake wakiltar karamar hukumar Nguru a jihar Yobe, wato Honarabul Musa Lawal Maja Kura, a cikin shekaru biyu kacal da hawan sa kujerar amma kun ga yadda rayuwarsa ta sauya. Nan hotunansa a lokacin da yake koyarwa a makaranta da sana'ar POS, da kuma bayan ya zama dan majalisa.
An baiwa Babban Bankin Najeriya, CBN shawarar fito da takardun kudi na Naira 20,000 da 10,000

An baiwa Babban Bankin Najeriya, CBN shawarar fito da takardun kudi na Naira 20,000 da 10,000

Duk Labarai
Wata kungiya me suna Quartus Economics ta bada shawara ga babban bankin Najeriya da ya fito da takardar kudin Naira 20,000 da 10,000. Kungiyar tace dalili kuwa shine a yanzu takarar Naira 1000 bata iya sayen wani abin a zo a gani. Tace fito da manyan kudaden zai ragewa mutane wahalar daukar kudade da yawa wajan gudanar da kasuwanci. Ungiyar tace ba gaskiya bane abinda ake fada cewa idan aka fito da sabbin kudin zasu iya saka farashin kayan masarufi su tashi. Kungiyar tace darajar Naira ta lalace sosai.
Da Duminsa: Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saka harajin kaso 15 kan Man fetur da Gas

Da Duminsa: Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saka harajin kaso 15 kan Man fetur da Gas

Duk Labarai
Rahotanni daga fadar shugaban kasa na cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya amince ko ya saka hannu kan kudirin dokar saka Harajin kaso 15 cikin 100 akan man fetur da gas da ake shigowa dasu Najeriya. Sakataren shugaban kasar, Damilotun Aderemi ne ya dauki takardar kudirin dokar inda ya kaiwa hukumomin da lamarin ya shafa dan a fara zartas da wannan doka. Ana tsammanin wannan sabuwar dokar haraji zata kara farashin man fetur da akalla N0.99, kamar yanda The Cable ta ruwaito.
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayar da Umarnin a dawo a ci gaba da yin Gwajin Makamin kare dangi

Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayar da Umarnin a dawo a ci gaba da yin Gwajin Makamin kare dangi

Duk Labarai
Republican presidential candidate and former U.S. President Donald Trump looks on in the courtroom, as his criminal trial over charges that he falsified business records to conceal money paid to silence porn star Stormy Daniels in 2016 continues, at Manhattan state court in New York City, U.S., April 23, 2024. REUTERS/Brendan Mcdermid/Pool Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya baiwa ma'aikatar yaki ta kasarsa umarnin a dawo a ci gaba da gwajin makamin kare dangi, watau Nokiliya. Shugaban yace idan dai wasu kasashe zasu rika yin gwajin bai ga dalilin da zai hana kasar Amurka itama ta rika yin irin wannan gwajin ba. Saidai masu sharhi sun ce abinda suka fahimta shine shugaban ba yana nufin a rika harba makamin bane, yana nufin a rika gwadawa Duniya Kwajin kasar Amurka ne. Hakan...
Kasar Saudiyya zata gina Filin Kwallon kafa(Stadium) wadda babu irinta a Duniya

Kasar Saudiyya zata gina Filin Kwallon kafa(Stadium) wadda babu irinta a Duniya

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Kasar Saudiyya ta sanar da shirinta na gina filin Kwallon kafa( Stadium) wanda babu irinsa a Duniya. Filin za'a ginashi ne a sararin samaniya wanda masana suka ce zai yi nisan kafa 1,150 daga kasa. Sannan zai dauki mutane 46,000. Sannan za'a ginashine a shekarar 2032. Wannan na daga cikin kokarin kasar ta Saudiyya na samun daukar nauyin wasan cin kofin kwallin Duniya na shekarar 2034. Hakanan gina Filin zai ci kudi har dala Biliyan $1.