Friday, February 27
Shadow

Duk Labarai

CBN sun saka sabuwar dokar kayyade hadahadar kudi na POS kada ya wuce Naira Miliyan 1.2 a rana

CBN sun saka sabuwar dokar kayyade hadahadar kudi na POS kada ya wuce Naira Miliyan 1.2 a rana

Duk Labarai
Babban bankin Najeriya, CBN ya saka sabbin dokokin hadahadar kudi na POS. CBN ya bayyana sabbin dokokin wanda yade dolene kowa da lamarin ya shafa ya tabbatar yana wa dokokin Biyayya. Daya daga cikin dokokin da suka fi daukar hankali itace wadda tace a kullun an Amincewa dan POS ne yayi hadahadar kudi da bata wuce Naira Miliyan 1.2 ba. Wasu dai na ganin wannan doka da wuya ta yi aiki domin mutum daya zai iya mallakar POS daban-daban fiye da daya.
Dangote ya rage farashin Gas din Girki

Dangote ya rage farashin Gas din Girki

Duk Labarai
Matatar Man fetur ta Dangote ta rage farashin Man Fetur. A yanzu farashin yana akan Naira ₦760 ne kan kowane kilo maimakon Naira ₦810 da ake saye a baya. Sauran masu samar da gas din girki a Najeriya irin su Matrix da Ardova suna sayar da gas dinne akan farashin Naira ₦920 Su kuwa AY Shafa da NIPCO suna sayar da gas dinne akan farashin Naira ₦910. Su kuwa Stockgap Depot suna sayar da gas dinne a farashi Naira ₦950 kan kowacce Lita. Hakan ya bayyana cewa, Gas din Dangote shine mafi Arha a Najeriya. Ana ganin hakan zai iya tilasta sauran masu samar da gas a Najeriya suma su rage farashinsu.
Ji yanda Matar soja Lt. Samson Haruna ta aikashi Qiyama ta hanyar Babbaqeshi Qurmus

Ji yanda Matar soja Lt. Samson Haruna ta aikashi Qiyama ta hanyar Babbaqeshi Qurmus

Duk Labarai
Matar sojan Najeriya Lt. Samson Haruna ta kasheshi ta hanayar cimma nasa wuta bayan da fada ya kaure tsakaninsu. Lamarin ya farune a Bassey Barracks, dake Ibagwa, karamar hukumar Abak dake jihar Akwa-Ibom. Lamarin ya farune ranar Sept. 22, 2025. Sojan wanda likita ne, sun samu zazzafar muhawara da matarsa me suna Mrs. Samson Haruna wanda hakan yasa ta yi amfani da fetur ta babbakeshi. Sojan ya samu raukuna sosai inda nan da nan aka garzaya dashi zuwa Asibiti. Bayan da aka je Asibitin ya rasu acan. An kama matar inda yanzu haka ake kan bicikenta.
Kalli Bidiyon: An yaye jami’an tsaro na musamman guda 380 da za su yi yaki da masu kwacen waya a Kano

Kalli Bidiyon: An yaye jami’an tsaro na musamman guda 380 da za su yi yaki da masu kwacen waya a Kano

Duk Labarai
An kammala horaswa da kuma yaye jami'an hukumar KOSSAP da aka samar na musamman a jihar Kano da zasu rika yaki da kwacen waya. Jami'an su 380 an kammala yaye su ne a ranar Lahadi inda kuma zasu fara aiki nan ba da jimawa ba. An shafe sati biyu ana basu horo. Matsalar kwacen waya yayi kamari a jihar Kano inda ake kashe mutane ana kwace musu wayoyi.
Lauya ya garzaya kotu inda yake neman ta hana Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan tsayawa takarar shugaban kasa a 2027

Lauya ya garzaya kotu inda yake neman ta hana Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan tsayawa takarar shugaban kasa a 2027

Duk Labarai
Wani lauya me suna Johnmary JideObi ya shigar da karar tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan kan neman kotu ta hanashi tsayawa takarar shugaban kasa a 2027. Ya shigar da karar ne ranar Litinin a babbar kotun tarayya dake Abuja. Yace idan Goodluck Jonathan ya sake cin zabe zai yi shekaru fiye da 8 da doka ta yadda kowane shugaba yayi. Dan hakane yake neman a hanashi tsayawa takarar shugaban kasa a 2027.
Najeriya na sa ran haƙo gangan ɗanyen mai miliyan1.8 a kullum

Najeriya na sa ran haƙo gangan ɗanyen mai miliyan1.8 a kullum

Duk Labarai
Shugaban kamfanin mai na Najeriya, NNPCL, Bayo Ojulari, ya bayyana kyakkyawan fatan cewa ƙasar zata dinga haƙo gangan ɗanyen mai miliyan1.8 kafin ƙarshen shekarar 2025. Kafar watsa labarai ta Channels TV ta ce shugaban kamfanin ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi, yayin da ya ke sanar da shugaba Bola Tinubu kan ayyukan kamfanin a jihar Legas. Mista Ojulari ya ce gyare-gyaren da suka yi a watannin Agusta da Satumba zasu taimaka wurin samar da ci gaba a wannan watan. Inda ya ƙara da cewa “Muna fatan kafin ƙarshen shekarar nan mu kai ga haƙo aƙalla gangan ɗanyen mai miliyan ɗaya da dubu 800 a kullum. ” A halin yanzu dai ƙasar na haƙo ganga miliyan 1.71 a kullum. Kuma ta kasance ɗaya daga cikin ƙasashen da ke gaba-gaba wurin samar da ɗanyen mai a ƙungiyar OPEC a duniya....
Bincike ya samu Ministan kimiyya na Najeriya da ‘mallakar takardun boge’

Bincike ya samu Ministan kimiyya na Najeriya da ‘mallakar takardun boge’

Duk Labarai
Wani bincike da jaridar Premium Times ta yi ya nuna cewa ana zargin ministan kimiyya da fasaha na Najeriya, Uche Nnaji, da yin takardun kammala karatu na boge, lamarin da ke ci-gaba da janyo cece-kuce a ƙasar. Binciken da jaridar ta Premium times ta wallafa ya ce an gano cewa ministan ya miƙa takardun bogin ga majalisar dattawan ƙasar domin tattance shi, bayan shugaban Bola Ahmed Tinubu ya miƙa sunansa cikin waɗanda yake so ya bai wa muƙamin minista a shekarar 2023. Jaridar ta yi ikirarin cewa takardun shaidar kammala karatun digiri da na bautar ƙasa na Mr Nnaji duka na boge ne. Inda ta ƙara da cewa masu suka sun ce ministan bai kammala karatun digirin ba, haka kuma takardar shaidar bautar ƙasar da ya miƙa wa ofishin sakataran gwamnatin tarayya da hukumar tatta...
Tinubu ya buƙaci NAHCON ta rage kuɗin Hajjin bana

Tinubu ya buƙaci NAHCON ta rage kuɗin Hajjin bana

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya buƙaci hukumar jin daɗin alhazai ta Najeriya NAHCON da ta rage kuɗin Hajjin bana, inda ya buƙaci hukumar ta fito da sabon kuɗin nan da kwana biyu. Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ne ya bayyana wannan buƙatar a ganawarsa da shugabannin hukumar a fadar gwamnatin ƙasar da ke Abuja a ranar Litinin. Ya yi kira da a samu ƙarin haɗin kai tsakanin hukumar a matakin ƙasa da takwarorintna na jihohi ciki har da gwamnoni domin a samu sauƙin gudanar da aikin Hajjin na bana. Da yake ganawa da manema labarai bayan taron, mataimakin shugaban ma'aikatan fadar shugaban ƙasa, Sanata Ibrahim Hadejia ya ce an yi taron ne domin ƙarƙare shirye-shiryen Hajjin na bana, ciki har da tattaunawa game da kuɗin kujera. "Saboda yadda farashin naira ya haɓaka da k...