Sunday, March 22
Shadow

Duk Labarai

An takewa Maiwushirya hakkinsa da aka tursasa masa sai ya auri ‘YarGuda>>Inji Gfresh Al-amin

An takewa Maiwushirya hakkinsa da aka tursasa masa sai ya auri ‘YarGuda>>Inji Gfresh Al-amin

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ya bayyana cewa, an takewa Maiwushirya hakkinsa da aka tursasa masa sai ya auri 'YarGuda da suke Bidiyo tare. Kotu dai ta baiwa Maiwushirya da 'YarGuda damar su yi aure inda tace idan hakan ya tabbata ba za'a dauresu ba. Gfresh Al-amin a cikin Bidiyon da ya sai ta shafinsa na Tiktok yace to kenan duk sauran mutane dake fim da mata sai ace sai sun auresu. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7563446093678218514?_t=ZS-90j7jprxrl3&_r=1
Lauya da ya halarci zaman Kotun inda aka yi shari’ar Maiwushirya da ‘YarGuda yace kotun ba tursasa musu aure ta yi ba, sune suka ce suna son yin aure shine kotu tace to tunda hakane ta yafe musu laifin da suka yi

Lauya da ya halarci zaman Kotun inda aka yi shari’ar Maiwushirya da ‘YarGuda yace kotun ba tursasa musu aure ta yi ba, sune suka ce suna son yin aure shine kotu tace to tunda hakane ta yafe musu laifin da suka yi

Duk Labarai
Wani lauya da ya halarci zaman shari'ar Maiwushirya da 'YarGuda yace ba kotu ce ta tilasta musu yin aure ba. Yace sune da kansu suka ce suna son auren juna dan haka kotu tace tunda hakane ta yafe musu laifin da suka aikata. Kalli Jawabinsa a kasa:. https://www.tiktok.com/@barristernurafuntua/video/7563390138827541780?_t=ZS-90ib3xSYy6T&_r=1
Duk da abinda nake yi ake zhaghina da zan fito ince zan yi aure mata sai na ture>>Inji Shahararren me wakar Bhatsaa>>Soja Boy

Duk da abinda nake yi ake zhaghina da zan fito ince zan yi aure mata sai na ture>>Inji Shahararren me wakar Bhatsaa>>Soja Boy

Duk Labarai
Tauraron me wakokin batsa da 'yan mata tsirara-tsirara, Soja Boy ya bayyana cewa duk da zagin da ake masa kan wakokinsa, da zai fito yace zai yi aure mata sai ya ture. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi ta kai tsaye a Tiktok inda aka tambayeshi ko ya zai so matar da zai aura ta amince ya ci gaba da abinda yake yi? Yace ko da bai samu matar aure ba anan Najeriya, zai iya zuwa kasashen Turawa ya yi aure. Amma yace anan ma duk da zagin da ake masa idan ya fito neman aure yasan mata sai ya ture.
Kalli Bidiyo: Bayan zaman da muka yi da majalisar Shura, ‘Yan Jarida sun gaya min cewa Wallahi basu yi tsammanin zan iya kare kaina ba>>Inji Malam Lawal Triumph

Kalli Bidiyo: Bayan zaman da muka yi da majalisar Shura, ‘Yan Jarida sun gaya min cewa Wallahi basu yi tsammanin zan iya kare kaina ba>>Inji Malam Lawal Triumph

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Malam Lawal Triumph ya bayyana cewa, 'yan jaridar da suka halarci wajan zaman majalisar shura sun bayyana cewa an aika su ne su cimma wata manufa. Yace sun gaya masa cewa wallahi ko kusa basu yi tsammanin zai iya kare kansa kan kalaman da yayi ba. Malam ya bayyana hakane a yayin da ya ci gaba da wa'azi bayan ya kare kansa a gaban majalisar Shura. https://www.tiktok.com/@zaidou1taza/video/7563395668383976760?_t=ZS-90iU0L8CIkb&_r=1
Kotu Ta ce a daura auren Maiwushirya da ‘yarGuda nan da kwanaki 60

Kotu Ta ce a daura auren Maiwushirya da ‘yarGuda nan da kwanaki 60

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Kano na cewa kotu ta bayar da umarnin a daura auren Maiwushirya da Habashiya 'yar guda nan da kwanaki 60. Mai Shari'a Halima Wali ce ta yi wannna hukunci bayan samunsu da laifin yada Bidiyon badala. Saidai 'yar Guda tace idan ba Maiwushirya na da gidan kansa ba, ba zata aureshi ba. Tuni dai Rahotanni suka ce an bude asusun neman taimako dan daura musu auren
Subhanallahi: Tauraruwar Tiktok Habiba Dorayi na shan ruwan Allah Wadai saboda sabon Bidiyon bhatsaa da ta yi

Subhanallahi: Tauraruwar Tiktok Habiba Dorayi na shan ruwan Allah Wadai saboda sabon Bidiyon bhatsaa da ta yi

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok Habiba Dorayi na shan tofin Allah tsine da Allah wadai saboda Bidiyon da ta yi tana rike da nonuwanta tana kalaman batsa. Ta yi Bidiyon ne a wani Tiktok live da suka yi ita da kawarta. Tace Nonuwanta suna da nama sosai inda tace lokacin da aka kaita Budurwa gidan Mijinta, bai iya tabawa ba, yana tabawa tana jin zafi. Wadannan kalamai nata sun jawo Muhawara da Allah wadai. https://www.tiktok.com/@zaima_wan/video/7563277148627258644?_t=ZS-90iD4rcfc5x&_r=1
Kungiyar Kwadago, NLC tace ta baiwa Gwamnatin Tarayya Sati 4 ta daidaita da Kungiyar malaman jami’a ta ASUU ko duka ma’aikatan Najeriya su tsunduma yajin aiki

Kungiyar Kwadago, NLC tace ta baiwa Gwamnatin Tarayya Sati 4 ta daidaita da Kungiyar malaman jami’a ta ASUU ko duka ma’aikatan Najeriya su tsunduma yajin aiki

Duk Labarai
Kungiyar Kwadago ta kasa, NLC ta gargadi Gwamnatin tarayya da cewa, ta basu sati 4 su daidaita da kungiyar malaman jami'a ta ASUU. Kungiyar tace idan kuwa ba'a samu daidaiton ba to suma zasu tsunduma yajin aiki su taya kungiyar ASUU din. Shugaban kungiyar NLC, Joe Ajaero ne ya bayyana haka ga manema labarai a Abuja inda yace kuma suna Allah wadai da kin biyan ma'aikatan ASUU din albashi saboda su shiga yajin aiki. Yace ba zasu kara bari a wulakanta wata kungiyar Kwadago ba suna gani.