Gidajen Talakawa Milyan Biyar Ne Suka Amfana Da Tallafin Naira Bilyan 493 Da Shugaba Tinubu Ya Raba”>>Inji Gwammati
"Gidajen Talakawa Milyan Biyar Ne Suka Amfana Da Tallafin Naira Bilyqn 493 Da Shugaba Tinubu Ya Raba".
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya cire takunkumin da aka saka kan asusun Hukumar Shirin Zuba Jarin Jin Kai ta Ƙasa “National Social Investment Programme Agency (NSIPA)”, wanda ya kai ga sakin sama da Naira biliyan 493 domin tallafawa gidaje miliyan biyar a fadin ƙasar. Tun a ranar 8 ga Janairu, 2024 ne aka dakatar da Ministar Harkokin Jin Kai da Rage Talauci, Dr Betta Edu, tare da umartar Hukumar Yaƙi da Laifukan Tattalin Arziki da Kuɗi (EFCC) ta gudanar da bincike kan duk wasu harkokin kuɗi na ma’aikatar da hukumomin da ke karkashinta. Haka kuma, Shugaban Ƙasa ya kafa kwamiti karkashin jagorancin Ministan Kudi, Wale Edun, domin duba tsarin kuɗi na shirin jin kai da inganta shi do...








