Thursday, March 5
Shadow

Duk Labarai

Idan Tinubu ya sake cin zabe, Najeriya ba zata kai Labari ba, Inji Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Idan Tinubu ya sake cin zabe, Najeriya ba zata kai Labari ba, Inji Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
TIRƘASHI: Zai yi Wuya Nijeriya ta Ci Gaba da Rayuwa Idan Tinubu ya Zarce a 2027 - El-Eufai Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, kuma Korarren Ministan da majalisa ta ƙi tantance wa, Malam Nasir El-Rufai , ya bayyana cewa makomar Najeriya na cikin hadari idan jam’iyyar APC ta ci gaba da mulki bayan 2027. Jaridar Sahara Reporters ta rawaito cewa El-Rufai ya bayyana hakan ne a Sakkwato yayin wani gangamin wayar da kan jama'a na jam’iyyar hamayya ta hadaka, African Democratic Congress (ADC), inda ya ce yana cikin siyasa ne don ceto kasa, ba don wata riba ba. Ya ce ya fice daga APC ne saboda gazawarta wajen tafiyar da mulki, yana mai gargadin cewa ci gaban mulkin APC zai iya rusa tubalin zamantakewa na kasar. El-Rufai, wanda yanzu ke daya daga cikin jiga-jigan ADC, ya sha alwashin hada ...
Kalli Bidiyo: Lokacin ina da kudi, matana 4 amma dana Talauce duk sun barni>>Inji Mai Dawayya

Kalli Bidiyo: Lokacin ina da kudi, matana 4 amma dana Talauce duk sun barni>>Inji Mai Dawayya

Duk Labarai
Tauraron mawakin Hausa, Aminu Mai Dawayya ya bayyana cewa a lokacin yana da budi, matansa 4. Ya bayyana hakane a wata hira da RFIHausa suka yi dashi. Ya bayyana cewa, Amma da kudinsa suka kare, duk sai kowa ya tafi ya barshi Yace Asalin dalilin da yasa ake ce masa Mai Dawayya shine shi masoyin Rukayya Dawayya ne da Ali Nuhu kuma asalin sanarsa Achaba ne. https://www.tiktok.com/@rfi_ha/video/7534272889013554488?_t=ZS-8ya2tLAjmzo&_r=1
Serap ta ba wa gwamnan Neja wa’adin janye umarnin rufe rediyon Badeggi FM

Serap ta ba wa gwamnan Neja wa’adin janye umarnin rufe rediyon Badeggi FM

Duk Labarai
Ƙungiyar neman shugabanci na gari ta Serap ta bai wa gwamnan jihar Neja da ke arewacin Najeriya wa'adin awa 48 domin ya janye umarnin rufe gidan rediyon Badeggi FM ko kuma ya fuskanci matakin shari'a. Cikin wata wasiƙa da ƙungiyar ta aika wa Gwamna Umaru Bago, shugaban Serap Kolawole Oluwadare ya ce rufe gidan rediyon da ke birnin Minna "saɓa wa doka" ne, kuma ya nemi gwamnan ya mayar musu da lasisinsu. "Toshe bakin masu suka da sunan tsaron ƙasa keta rantsuwar kama aiki da ka yi ne da kuma ɓata sunan Najeriya a idon duniya game da haƙƙin ɗan'adam," a cewar wasiƙar. A ranar Juma'a ne Gwamna Bago ya bayar da umarnin rufe gidan rediyon na Badeggi FM nan take tare da ƙwace lasisinsa saboda zargin "tayar da fitina".
Kalli Bidiyo: Abin takaici ne yanda aka baiwa ‘yan mata ‘yan kwallon Najeriya kyautar Naira Miliyan 160, kudin da har soja ya gama aikinsa in za’a hada duka abinda zai samu ba zai kai hakan ba>>Soja ya koka

Kalli Bidiyo: Abin takaici ne yanda aka baiwa ‘yan mata ‘yan kwallon Najeriya kyautar Naira Miliyan 160, kudin da har soja ya gama aikinsa in za’a hada duka abinda zai samu ba zai kai hakan ba>>Soja ya koka

Duk Labarai
Sojan Najeriya ya koka bisa yanda aka baiwa 'yan mata 'yan kwallon Najeriya kyautar Miliyoyin kudade da gidaje bayan sun lashe kofij gasar kwallon mata ta Afrika. Sojan yace duka aikin da suka yi bai wuce na watanni 3 ba. Yace amma abin takaici shine kudaden da aka basu tun daga randa aka dauki soja aiki har ya gama aikinsa ba zai samu irin wadannan kudaden ba. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1951970780218060823?t=T8tOwYdS5fcx3MI5pgmKZQ&s=19
Gwamnati za ta gyara tsarin birnin Maiduguri domin kare ambaliya

Gwamnati za ta gyara tsarin birnin Maiduguri domin kare ambaliya

Duk Labarai
Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce gwamnatinsa ta fara yunƙurin gyara tsarin birnin jihar domin kiyaye jihar daga ambaliya. Zulum ya bayyana haka ne jim kaɗan bayan ziyarar gani da ido da ya yi wajen gyara da ake yi a dam ɗin Alau, inda ya ce har yanzu akwai wasu da suke gini a magudanan ruwa da kuma masu zuba shara suna toshe magudunan ruwa. "Za mu duba tare da gyara tsarin birnin Maiduguri domin mu tabbatar dukkan magudanan ruwanmu a buɗe suke kuma suna aiki," in ji shi kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito. Ya yi gargaɗin cewa duk wani gini da aka yi a magudunan ruwa za a rushe su. Ya ce za su ɗauki matakin rusau ɗin ne domin kare sake aukuwar irin ambaliya da ta auku a ranar 10 ga watan Satumban 2024 a Jere da ke Maiduguri. A game da fargabar d...
Ku zabeni, na yi Alkawarin wa’adi daya kawai zan yi in sauka>>Peter Obi

Ku zabeni, na yi Alkawarin wa’adi daya kawai zan yi in sauka>>Peter Obi

Duk Labarai
Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter Obi ya ce idan ya samu nasarar zama shugaban ƙasar, wa'adi ɗaya na shekara huɗu kawai zai yi kamar yadda ya yi alƙawari. Obi ya bayyana haka ne a shafinsa na X, inda ya ce ko tsohon shugaban Amurka, Abraham Lincoln wa'adi ɗaya ya yi na shekara huɗu, "sannan John F. Kennedy bai ma ƙarasa wa'adi ɗaya ba, amma ana cigaba da tunawa da su a matsayin shugabanni masu adalci." Ya ce ko a Afirka, Nelson Mandela ya zama abin koyi a duniya wajen shugabanci na adalci, "amma wa'adi ɗaya kawai ya yi." "Ba daɗewa a ofis ba ne ke alamta nasara, irin ayyukan da shugaba ya yi ne za a riƙa tunawa. Saboda haka ne nake sake nanata alƙawarin da na yi cewa wa'adi ɗaya na shekara huɗu kawai zan yi idan na zama shugaban Najeriya," in ji shi...
ABIN A YABA: Ya Tara Marayu Sama Da 200 Ya Yi Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa Tare Da Su, Inda Ya Yi Wa Kowannensu Dinki

ABIN A YABA: Ya Tara Marayu Sama Da 200 Ya Yi Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa Tare Da Su, Inda Ya Yi Wa Kowannensu Dinki

Duk Labarai
ABIN A YABA: Ya Tara Marayu Sama Da 200 Ya Yi Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa Tare Da Su, Inda Ya Yi Wa Kowannensu Dinki …samun matashi irin Hon. Muhammad Sulai Yaro abu ne mai wuya Tabbas samun matashi kamar Hon Muhammed Sulai Yaro wanda aka nada shi a matsayin Dan Gatan Girei abu ne da kamar wuya, matashi ne da ya mayar da hankalin sa kan takalawa. A jiya ne dai ya yi bikin zagayowar ranar haihuwar sa, inda ya debi yara marayu sama da dari biyu ya yi musu sabon dinki, kuma ya hada musu liyafa, har saida ya zubar da hawaye a wajen. Haka kuma ya yi musu alkawari zai ci gaba da tallafa musu har karshen rayuwar su. Wace fata za ku yi masa? Daga Hon Ishaq B Aliyu