Saturday, December 13
Shadow

Duk Labarai

Ba wanda yake da hujja kan mijina (Abacha) ya saci kuɗin Najeriya, kuma bai soke zaɓen Abiola ba – in ji Maryam Abacha

Ba wanda yake da hujja kan mijina (Abacha) ya saci kuɗin Najeriya, kuma bai soke zaɓen Abiola ba – in ji Maryam Abacha

Duk Labarai
Uwargidan marigayi tsohon shugaban Najeriya, Maryam Abacha, ta musanta zargin da ake yi wa mijinta, tsohon shugaban ƙasa na mulkin soji, Janar Sani Abacha, kan zargin satar kuɗin Najeriya. Abacha ya yi mulkin Najeriya ne daga shekarar 1993 zuwa 1998 kuma ya rasu ne a ranar 8 ga Yunin 1998. DailyTrust ta rawaito a cikin wata hira da gidan talabijin ɗin TVC ya yi ta yi a ranar Lahadi kan cikar Abacha shekaru 27 da rasuwa, uwargidan marigayin ta ce kuɗin da ake zargin mijinta ya sata, ba satar su ya yi ba, kawai ana yi masa mummunar fassara ce. A cikin waɗannan shekarun baya-bayan nan, gwamnatoci daban-daban sun sanar da gano miliyoyin kuɗin dalar Amurka a asusan ƙasashen waje waɗanda ake wa laƙabi da “Abacha loot.” Waɗannan kuɗaɗe, an dawo da su daga ƙasashen Switzerland da Amurk...
Gwamnatin Jihar Neja Ta Bada Tallafin Naira Bilyan Daya Ga Wadanda iftila’in Ruwa Ya Shafa A Garin Mokwa

Gwamnatin Jihar Neja Ta Bada Tallafin Naira Bilyan Daya Ga Wadanda iftila’in Ruwa Ya Shafa A Garin Mokwa

Duk Labarai
Gwamnatin Jihar Neja Ta Bada Tallafin Naira Bilyan Daya Ga Wadanda iftila’in Ruwa Ya Shafa A Garin Mokwa. A yau ne Gwamna Bago ya bayyana haka a daidai lokacin da ya ziyarci garin, inda ya bukaci mazauna yankunan dake kusa da kogin da su kaura, sannan ya ba su filaye su gina da tallafin kudin da ya ba su. Daga Rashida Bala Suleja
Ka Daina Boye-Boye Ka Fito Fili Ka Koma Jam’iyyar APC, Matawalle Ga Gwamnan Zamfara

Ka Daina Boye-Boye Ka Fito Fili Ka Koma Jam’iyyar APC, Matawalle Ga Gwamnan Zamfara

Duk Labarai
Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, kuma tsohon Gwamnan jihar Zamfara, Dr. Bello Mohammed Matawalle, ya bukaci Gwamna mai ci, Dr. Dauda Lawal, da ya fito fili ya bayyana cewa ya shiga jam’iyyar APC ya daina wani boye-boye. Da yake jawabi a gidansa da ke Maradun yayin wata ziyarar gaisuwar Sallah da dubban magoya baya suka kai masa, Matawalle ya ce lokaci ya yi da Gwamna Lawal zai daina “kumbiya-kumbiya" yana rufa-rufa” ya fito fili ya bayyana matsayarsa a jam'iyyance. “Kofar jam’iyyarmu a bude take ga duk wanda ke neman ci gaban gaskiya ga jihar Zamfara da Nijeriya,” inji Matawalle, yana mai jaddada cewa bai dauki komai a ransa ba dangane da zabin siyasar Gwamna Lawal. Ya ce APC jam’iyya ce da ke kan turbar tawali’u, gaskiya da shugabanci nagari. “Muna kira gare shi ya ...
‘Idan ba a yashe Alo Dam ba za mu iya fuskantar matsala a Borno’

‘Idan ba a yashe Alo Dam ba za mu iya fuskantar matsala a Borno’

Duk Labarai
Gwamnatin jihar Borno ta yi kira ga gwamnatin shugaba Tinubu ta hanzarta daukar mataki kan ɗan kwangilar da ta baiwa aikin yashe dam din Alou da ya haifar da ambaliya a bara. Ta ce duk da cewar sun yashe wani sashe na dam din amma, har yanzu akwai babbar barazana da za a iya fuskantar mumunar ambaliya. Kwamishinan yaɗ labarai da harkokin tsaro na jihar Borno, Farfesa Umar Tar da harkkokin tsaro ya shaida wa BBC cewa an bayar da kwantaragin kuma minista ya je ya ƙaddamar da aikin. "Har yanzu ba mu ga ƴan kwangila sun zo domin fara aikin ba kuma yanzu ga damuna ta riga ta sauka. Idan ba a yi aikin nan da wuri ba to idan ruwa ya zo ya yi halinsa to lallai za a samu matsala. Ya kamata ace an yashe ruwan saboda irin cunkushewar da ya yi. Idan aka yashe shi to ko ruwa ya zo da yawa ba z...
Ƴansanda sun kama mutum 27, sun ƙwàtò màggàn màkàmài a Kaduna

Ƴansanda sun kama mutum 27, sun ƙwàtò màggàn màkàmài a Kaduna

Duk Labarai
Ƴansanda a jihar Kaduna sun ce sun kama mutum 27 waɗanda ake zargi da aikata laifuka daba-daban. Wata sanarwar da mai magana da yawun ƴansandan jihar DSP Mansir Hassan ya fitar, ta ce an samu nasarar kama ɓata-garin ne bayan wani samame da ta kai maɓoyarsu a yankin Kawo. "Mun kai samamen ne jiya Lahadi a lungu da sako na yankin Kawo. Abin ya kai ga kama mutum 27 da ake zargi da aikata laifuka har ma da ƙwato muggan makamai," in ji Mansir. Ya ce cikin makaman da suka ƙwato sun haɗa da wuƙaƙe da adduna da fartanyu da kuma ƙunshin ganyayyaki da ake kyautata zaton tabar wiwi ce da kuma sauran kayan maye. Kwamishinan ƴansandan jihar, CP Rabiu Muhammad ya ƙara nanata ƙoƙarin rundunar wajen ganin an mutunta doka da oda a faɗin jihar. Ya ƙara da cewa Kaduna jiha ce mai zaman lafiya,...
Kaf masu neman takarar shugabancin Najeriya babu Gwani wanda ya cancanta kamar ni>>Inji Peter Obi

Kaf masu neman takarar shugabancin Najeriya babu Gwani wanda ya cancanta kamar ni>>Inji Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa a karkashin jam'iyyar Labour party a zaben shekarar 2027, Peter Obi ya bayyana cewa, babu Dimokradiyya a mulkin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Ya bayyana cewa idan aka lura da abinda ya faru a jihar Rivers da zaben jihar Edo za'a iya gane cewa, babu Dimokradiyya a Najeriya. Peter Obi ya bayyana hakane a wata ganawa da aka yi dashi a Arise TV. Yace shiyasa yake ta neman ya zama shugaban kasa, saboda ya gyara wannan matsalar, yace a kaf cikin masu neman takarar shugaban kasar, babu gwani wanda ke da kwarewa kamarsa saboda yayi aiki da kamfanoni kuma ya zama gwamna.
Wata Sabuwa: Kakakin Jam’iyyar PDP ya koma jam’iyyar APC

Wata Sabuwa: Kakakin Jam’iyyar PDP ya koma jam’iyyar APC

Duk Labarai
Kakakin jam'iyyar PDP a jihar Legas, Hakeem Amode ya koma jam'iyyar APC. Ya bayyana hakane a wata ganawa da manema labarai tare da masoyansa a Ikeja ranar Litinin. Sun bayyana cewa, tsohon shugaban jam'iyyar PDP na jihar, Abdul-Azeez Adediran (Jandor), da ya koma APC ne ya dauki hankulansu suka koma jam'iyyar APC. A jawabinsa yace duka jam'iyyar PDP a jihar daga sama har kasa sun koma APC inda yace saboda jam'iyyar PDP ta tasa alkibla.
An kaddamar da shafin Yanar gizo na masoya Shugaba Tinubu, da ke da ra’ayin sake zabensa a 2027 duk wanda ke da ra’ayi yana iya zuwa yayi rijista

An kaddamar da shafin Yanar gizo na masoya Shugaba Tinubu, da ke da ra’ayin sake zabensa a 2027 duk wanda ke da ra’ayi yana iya zuwa yayi rijista

Duk Labarai
Kungiyar masoya shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sun kaddamar da shafin yanar gizo na wadanda kw da ra'ayin sake zaben shugaban kasar a shekarar 2027. Kungiyar me suna the BAT Ideological Group ta bayyana cewa, ta yi hakanne dan hada bayanan masoya shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da wanda suke son sake zabensa. Kungiyar tace kuma hakan zai saukaka maganar ace sai mutum ya je Abuja dan za'a yi meeting ko dan zai yi rijista. Tace kuma hakan zai saukaka mata yada manufar shugaban kasar ga al'umma. Shugaban kungiyar, Bamidele Atoyebi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.
An kama wannan mutumin ya saci kwalayen sigari guda 9 daga wani Super Market wanda darajarsu ta kai Naira Dubu 90

An kama wannan mutumin ya saci kwalayen sigari guda 9 daga wani Super Market wanda darajarsu ta kai Naira Dubu 90

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, jami'an tsaro a jihar Legas karkashin rundunar RRS dake Falomo a Ikoyi sun kama wani mutum da kwalayen sigari guda 9 da ya sata daga wani babban shagon da ake cewa, Super Market. An kiyas ta cewa darajar kwalayen sigarin da ya sata zasu kai Naira Dubu 90. Hukumar 'yansandan tace ta kama wanda ake zarginne da misalin karfe 5:30 pm na yammacin ranar Labadi. Hukumar 'yansandan tace kowane kwalin sigari ana sayar dashi akan Naira dubu 10 wanda jimulla kudin sigarin da ya sata Naira dubu 90 kenan. Sunce Tuni suka mikashi ga hukumar 'yansanda ta Falomo.
Karya Ake min, ni bance ‘yan Bìndìgà sun kaiwa Janar Buratai hari ba>>Inji Sanata Ali Ndume

Karya Ake min, ni bance ‘yan Bìndìgà sun kaiwa Janar Buratai hari ba>>Inji Sanata Ali Ndume

Duk Labarai
Sanata Ali Ndume daga jihar Borno ya bayyana cewa, karya ake masa shi baice an kaiwa tsohon shugaban sojojin Najeriya, Janar Tukur Yusuf Buratai hari ba. Rahotanni sun watsu cewa, Sanata Ali Ndume ya ce an kaiwa Buratai hari a ranar Juma'ar data gabata inda ya tsallake rijiya da baya. Saidai a bayanin Sanata Ali Ndume bayan da wancan labari ya watsu shine shi bai ce haka ba, cewa yayi an kaiwa garin Buratai hari ne ba tsohon shugaban sojojin ba. Mayakan kungiyar dake ikirarin Jìhàdì ta Bòkò Hàràm dai sun dawo gadan-gadan inda suke kaiwa jami'an tsaro hare-hare akai-akai inda wasu rahotannin ke cewa ma sun fi sojojin Najeriya makaman yaki.